Hausa Novels and Stories

Yar Aikin Karuwai 28-29

Sponsored links

nace to Goodnight,rakoshi nayi har mota securities suna nan suna gadina,da kaina na bude masa motar ya Shige mota na rufe Masa glass ya sauke yace sai gobe nace Allah ya kaika lafiya ka kula da tuki na juya Ina cewa banda ganganci matarka zaka yiwa asara ni ba ruwana,Murmushi yayi kawai ya murza Kan motarsa yaIna komawa na Kira Seraline na fayyace Mata komai dake bama boyewa juna sirri,Sera tace to ai Kuwa zai iya zuwa bakatatan ya nemeki Kuma Kinga dai yanda muke kashewa Gomnatinmu kudi Kinga yanda muke Shan gyara uban kowa ya dandanaka bai iya barinka sai ya dawo,kina da kudi ki kawo a fara kashe dubu dari biyu haka a tsumaki karuwai basa Wasa da gyara Kai kusan kudinmu a gyaran jiki ke tafiya da haka muke samun riba jari muke zubawa ki kawo kudi a zubawa jikinki jari,in kana da kyau ka Kara da wanka karki kalli kina da kyau Wai kice baza ki Kara da wanka ba,nace ai shine na gani nima gobe Zan rokeshi ya barni nazo sai muje Sera ta kwashe da dariya naji dariyar su Wise ma a Wayar hahaha Sera tace kin gammu dukanmu yau Muna gida Hira akeyi suna jinki munce kin dakkowa kanki masifa,Star ce ta kwace Wayar tace Yar wanke wanken karuwai haka Kika jefa kanki a masifa sai kace mijinki zai wani hanaki fita baki da yanci ma wato sai ma ya baki izini zaki fito mene amfanin barikin da Kika shigo daga farawa shike nan sai ki tsaya kina bin Maganar katon banza,nace Kinga star ba katon banza bane karki sake zagar min bar gidan.

Duk da haka zugar tasu ta danyi tasiri a zuciyata amma na danne washe gari da Yamma yazo 5pm,na shirya cikin wata doguwar rigar nayi rolling da mayafinta na fito a gabansa na durkusa nace dan Allah ka barni naje na dawo wlh bazan dade ba wajen Sera zanje matsala ce ta taso a dakin da Muka Kama karya na sharara Masa,yace hour nawa Zan baki? Nace 3hrs ma yace karki wuce 9pm Baki dawo ba nace to Ina murna na fita ya kwanta Yana jirana,Ina fita na shiga taxi,a ciki na cire Abayata kana nan kayana da nazo dasu gidan Suka bayyana na saka hular gashi na Kar ma su Sera su ganni da manyan Kaya suyi min Dariya,a cikin jaka na saka su,suka ganni nazo Sera tace ya barki kenan nace ae tare da kwanciya a saman gadon nace tsakani da Allah na gaji da mutumin nan Sera,ya takurani ya hanani lekawa ko kofar gida gashi dole sai na sa manyan Kaya na rufe jikina,Kinga takura komai nayi zai ce ba kyau,musulunci kaza kaza gashi mugun tsoronsa nake ji Yana da wani kwarjini kyansa kadai ya Isa ya rudaka gashi baya dariya sosai inda kisan ubana haka ya takura min na karashe da Tsaki, Sera ta dinga dariya tace ke Kika ga Zaki iya ta jawo sigarinta ta kunna Mata wuta,Ina mita nace gida ba nishadi ba kida ba shanawa Ina cikin wahala ai wlh kwana nan na kusa gudowa barikina bazan iya ba,Sera tace maybe sonki fa yake dama kina son aure sai kiyi abinki,nace wa ai da ne nace Ina son aure yanzu Kam rabani da wahala bazan iya ba aure baya tsarina a dinga takura min bada ni ba amma daga ganin mutumin zai iya love,zabura nayi nace tashi mu tafi 3hours ya bani idan na wuce ba mutunci,Sera dariya Kamar ta kasheta tace maganinki kenan yanzu gwara ki hada kanki zo mu tafi gidan Hajiya Mazarkwaila,dariyar sunan ya kamani nace hala itama tsohuwar karuwa ce domin daga Jin sunan bana kirki bane,Sera tace ai muguwar tsohuwar karuwa ce har yanzu ma Kuma yanzu ta koma kawalci manyan masu kudi take kaiwa Mata gata uwar karuwai kayan maye ba Wanda bata siyarwa ta tara arziki da bariki attajira ce ta gaske Kuma tana gyaran jiki na Mata gyaran skin gyaran Gomnati in and out amma akwai kashe kudi amma fa ba karya da kayan kasar waje take amfani idan Namiji ya dandanaki wlh ko a gaban uwarsa in zai ganki sai hankalinsa ya tashi bai iya kusantar wata yaji nutsuwa sai ke,nace iceko ba shirka bace? Tsaki taja tace ance Miki maganin kasar waje na gargajiya kina shirme,kin San karuwai muma ba tsafin da bamayi idan Muka hadu da me kudin gaske wlh in Muka Masa wani tsafin shi da iyalinsa har abada kullum Yana bariki wajenmu, jira nake Allah ya hadani da wani gagararren me kudin uwarsa ma Sai ya juya Mata baya,baki na saki nace nidai ba ruwana wallahi bazan je ko gun Malam ba bare shirka Allah ka tsareni,Sera tace ameen karki isheni Karuwar banza Karuwar wofi,dariya nayi nace karuwai dai Sera har yau dadin sex din nan ban ji ba ban taba yi ba Ina ta ikararin karuwanci amma Abu ya gagareni,ganin dama Kika Yi kin biyewa Dan iskan farkanki Muna tafiya muna hira Muka shiga napep nace Sera nifa yanzu kin San me? tace Ina jinki nace sha’awa ce ta dameni kullum da ita nake kwana nake tashi,to kin cuci kanki kin zauna a gidan dan banza babu me dan saitaki ba dole ba Kuma kina bariki kullum dare da rana a maganganun batsa muke dole a dinga taso Miki da sha’awa Kar aje ayi gyaran jiki Kuma abin yayi Miki yawa Kawai a hakura da gyaran a siya Miki na infection da Wanda zai dai dan dawwamar Miki da niima Kar kizo ki afkawa maza,dariya nayi nace ai Kuwa da ce Masa zanyi idan yasan baya son sex to ya dinga saka wandon karfe dama naji Yana cewa kwanan nan da wandon karfe zai dinga zuwa gidan,dariya mukayi har Muka je gidan Mazarkwaila,gidane na gagara gidanta abin kallo ne Muka shiga tana Palo ita kadai tana kallo kana ganinta ba sai an fada maka ba kasan shedan ya gama fitsare Mata Kai muguwar Yar duniya ce.

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button