Hausa Novels and Stories

Yar Aikin Karuwai 26-27

Sponsored links

Washe gari bayan na gama gyara ko Ina na gidan na karya yau bai zo ba har Yamma sai magriba Ina ta kallon film yinin ranar gaba daya, da Magriba ya shigo bayan ya dawo daga masallaci,Ina ganinsa na fashe da kuka nace Allah ni tafiya zanyi gida na gaji da nan bana so ka ajiyeni a prison ni gidanmu Zan tafi Ina can cikin nishadi ka ajiyeni a nan ni bazan iya ba na nuna doguwar rigar da nasa me tsada cikin kayan da ya siya min tayi min mugun kyau nace kalli Riga har kasa gashi ni rigar ta dameni bana so,sai da na gama Ina tsaye a gabansa yace wannan aikin da kike ikirari kina fita Wai Dan me kike Yi? nace kudi yace to biyanki zanyi ba kyauta nace ki zauna ba,Ina goge hawayena na koma na zauna tare da turo baki gaba,kudi ya zaro dala dari dari guda uku ya Mika min Yace gashi,kallonsa nayi nace wata fa bai cika ba kace Kuma sai wata yace ae baki nayi ki Kara hakuri ya furta tare da Zama,mikewa nayi da murna na kasa magana ma nace wannan Kawai na roko ne akan na zauna Kuma idan wata yayi zaka bani albashi? Yace ae,nace yau ana burar….na dura ashar nace la’ilahaillahu Wai Kai to me kake amfana dani,baka taba ko nono na Kawai ka ajiyeni ka dinga biyana kudi every time money ehhhhheheh nayi wata mahaukaciyar dariya Ina tafa hannaye nace bafa ka amfanuwa da ni a Zamanin nan,na nuna kaina nace ni Kuma banza Rabi wai ni ka bawa Elizabeth, nace yehoho kai Nawwar zan iya maka bauta,Kai mutumin kirki ne Kawai gani ka bautar dani kayi abinda kaga dama dani,ko wuta ka fada Zan iya binka nima na wulla ciki,ah’ah ikon Allah,kallona yakeyi Yana ta dariya yanda na haukace akan kudi,gabansa na durkusa nace Alhaji dama dazu ban gaisheka ba Ina yini ya iyalin? ya kwashe da dariyar da ban taba ganin yayita ba,nace Dan Allah kunyarka nake ji kana ta min kyauta baka tabani bana Jin dadi wlh uhm Sana’a nake uhm haba dan Allah yanzu ko Yan nono baza ka taba ba,yace ae nace dan Allah da girmansu wlh Allah ya bani akwai auki hiiim suke,yace na gode,mikewa nayi nace shike nan Allah yasa dai matarka tana baka nata,a ransa yace ko ta bani ma Yan karamaye ne ko saurararsu banyi a fili yace Ina samun halak dina nace ai Kuwa ta kyauta amma idan ta maka hauka Kawai ka fada min naje naci babbar burar….,Wai karuwai ma irinmu muke badawa bare mace da mijinta mene amfaninta idan ba a ragargajeta ba shi yasa fa nayi hips kugu na ya bude to yau da gobe taki Wasa ana ta iban harka,yace Wai ke in tambayeki,nace Ina jinka na nutsu sosai yace bakya Jin kunyata? Kai na daga masa nace ae bana ji,sabo da me? ta gudu ai ni bani da kunya na gantalar a titi bana Jin kunyar uban kowa yau da gobe taki wasa,numfashi ya ja yace to idan nazo ki dinga kokarin Adana kalamanki na banza bana so ki daina Yi a gabana bana so tunda kince duk abinda nace kiyi zakiyi bana son kalaman banza,nace to zanyi Inshaallah na daina, better ya furta nace to mu koma karatu Mana,yace me Kika sani a addini da kina da ilimin addini ai da baki abinda kike ba sabo da a wani Hadisi Manzon Allah (SAW) yan acewa

kullu ummati yadkulunar jannata….kafin ya rufe baki na karbe Hadisin naci gaba da karanta Masa Ina fassarawa nace wato ka gane annabi (SAW) yace dukkan alummata zasu shiga aljana,sai yace illa man aba sai dai Wanda yaki kaga irin mu kenan munki mu tunda Muna karuwanci to Allah ya shirye mu,sai sahabbai Suka ce kalu ya rasulillahi,Suka ce ya ma’aikin Allah wa yam aba?waye zai ki? Sai ya basu amsa Wa man asani Wanda ya Saba mini faqat aba hakika yaki,Allah ya shirye mu na furta yace ameen,nace na kusa fa sauka nan daka ganni da ilimina ko a karatun Qur’ani baza ka kureni ba sannan Ina da littafa da dama a kaina sabo da Ina zuwa Islamiyya a kauye Kuma na dage a lokacin.

Wato kin sani kike take sani nace mu bar zancen kaga Ina so na sanarwa Kawata Seraline ta San Ina nan Kar tazo hankalinta ya tashi bata ganni ba har kwana biyu yace ki kirata a waya Mana ga wayarki nan, wayata na jawo na Kira Seraline tana dagawa tace Ina ta kiranki wayarki a kashe Ina Kika shiga duk mun damu su Wise sai gwada wayarki ake bata shiga? nace sorry dama Kira nayi na fada Miki Ina gidan Saurayin nan nawa da ya bani daloli to shine yace na zauna a gidan zai biyani na Dan tayashi kwana na wani lokaci shine nace bari na fada Miki ki fadawa mutanenmu kafin na dawo, Seraline ta Yi dariya tace kice kin Zama Yar Hannu nace ae Kawai Muka danyi surutun mu na Yan duniya sannan na kashe Wayar, nace ko Watarana baza kayi sex dani ba? ganin na dameshi sai yace sai Watarana Kawai Sanda naga dama zan iya ki kwantar da hankalinki ko yaushe Zan iya,ya tashi zai fita nace Ina zakaje daga shigowa zaka fita ni baza ka bani lokacina ba wai ni Allah Zan gudu gida na koma inda na fito,karamin Tsaki ya ja ya dawo ya zauna na kamo Mana Nigeria film Muna kaiwa suna saka sabo Muka ci gaba da kalla tare Muna sharhi a kai,cikin Raina Kuwa tunani nake Yi yace ko yaushe zai iya sex dani gashi ni ba taba Yi nayi ba,na dai Saba da maza arna da Yan daudu zamu rungume juna Babu batun mace ko Namiji har zama muke a cinyar Namiji Kamar mace Yar uwarka,a raina nace idan yazo ko yaushe banyi gyaran jiki bafa yazo ya jini ba Dadi ai dole na Kira Sera ya Zama idan bani ya kusanta ba bazai ji Dadi ba tunda dai nasa ran Zan Fara Ashawo work idan ma zai na biyana ko yaushe ai ba matsala sai na dinga Yi da shi Kawai mutum daya,Ina ta sake sake a raina har ya Fara Jin bacci a nan yayi Sallah ya mike yace matata tana jirana

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button