Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 53

Sponsored links

Dariya ce takecin fatima zainab sosai tadai daure ta cigaba da kukan munafurci zuciyarta cike da mamakin yanda daddy ya karbi auren hannu bibbiyu, anya kuwa? anya ba wata a kasa? Kai koma menene bazata hakura ba sai tafitar da mama daga gidan…… Tana cikin wannan tinani tajuyo muryar mama na iwun:

“Wallahi bazata saku ba, duk wahalar danasha kafin na shawo kanka bazata tafi a banza ba wallahi, kasan ko nawa na kashe? Kai wallahi yau saidai ka zaba ko ni ko wannan tsinannan auren cin amanar da kuke shirin yi!”….

“Au gurin mallamai dama kike kaini, yasa bana gane kaina wataran”?

“Kwarai kuma ba abinda ka isa kayi dan na gama dakai, sai yanda nayi da kai, saboda haka ka janye aurennan kona bar maka gida!”….

“Allah ya toni asirinki muguwa azzaluma, wannan auren kuma ba fashi, saiki tattara yanaki yanaki ki barmin gida, na tsinke igiya dayan daya rage a tsakaninmu, kije na sakeki! Na baki minti uku ki kwashi tarkacenki ki barmin gida, karki sake ki tafimin da ya’ya kuma”….

 

Wani mahaukacin ihu mama ta rusa da hatta megadi dake chan bakin gate saida ya jiyota,jin abun tayi kamar saukar aradu, ko a mafarki bata taba kawowa zasu kara rabuwa da daddy ba musamman yanda take tinanin aikin da mallaminta ya mata na cin shi sosai, a haukarta kuma in kayiwa mutum asiri zaka iya fadamasa tinda kariga ka gama dashi, sai gashi alhaji ya tsinke igiya dayan da take takama dashi abu kamar almara? ganin fa wankin hula na neman kaita dare yasata tsugunawa tana fadin;

“Dan Allah dan Annabi alhaji ka fadamin mafarki nake baka sakeni ba, inka rabu dani ina zan nufa”…..

A hassale yace;

 

“Ki nufa duk inda kikaso mana, in bakiji sosai ba bari in kara maimaita miki, na sakeki saki uku hafsah!!!”…

 

Sai ganin mama kawai sukayi a sume tsabar gigicewar datayi, sai a lokacin su husnah dake labe sunata kuka sukayo kanta da sauri suna jijjigata…..

Fatima zainab ko ganin ankashe boss yasata zamewa sadap sadap ta gudu daga part din, tabar gidan gabadaya, a ranta tana fadin ko banza kwalliya ta biya kudin sabulu, ko a iya haka aka tsaya anbiyata….

Convoy din wasu zafaffan Louis Vuitton ne suka sharo a guje, duk inda sukabi sai an kallesu saboda kana gani kasan ba karamin mutum bane a ciki, basu tsaya a ko ina ba sai a unguwar Asokoro dayake cikin garin abuja, a gaban wani hadadden mansion sukayi parking suka shiga yin horn… Sun jima suna horn kafin wani security ya fito ya tambayesu visiting or appointment letter dinsu dame gidan, dukda yasan ba kananan mutane bane saidai doka ce me karfi baa shiga gidan without permission!, wani bodyguard ne yayiwa security din bayanin wanda yazo ganin me gidan, ce mishi yayi ya danyi holding on yana zuwa…

 

Juyawa yayi ya koma ciki, landline din daze sadasa da me gidan directly in tana kusa ya kira, saida yayi ringing sau uku sannan aka dauka, bayani ya mata tace ‘ok a barsu su shigo’……

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button