Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 54

Sponsored links

Juyawa yayi ya koma ciki, landline din daze sadasa da me gidan directly in tana kusa ya kira, saida yayi ringing sau uku sannan aka dauka, bayani ya mata tace ‘ok a barsu su shigo’……

 

Bude musu gate akayi suka shiga, duk yawan motocinsu saida parking space din ya daukesu harda sauran space banda tarin motocin dake jibge a gidan….

 

Dakatar da bodyguards dinsa yayi daya daga cikin securities din gidan yayi leading dinsa to guest part…

 

Yana zama wata maid tazo ta cika gabansa da kayan ciye ciye, dan haka tsarin gidan yake indai akwai bako ko baki a guest part zaayi cika gaban mutum da abubuwa, haka aka kai bodyguards dinsa garden suma aka cikasu da kayan ciyeciye, suka bararraje sunaci suna hirarsu abunsu…..

 

Tinda aka kai Dad part guest part din mami yake bin parlourn da kallo yana mamakin yaushe ta bunkasa haka?, ashe dole rashin mutunci ya karu tinda tana cikin daula haka? Bawai befi karfin duk abinda yake parlourn bane saidai betaba expecting ze ganta a cikin mansion haka ba, address din gidanma saida yasha wahala kafin ya samu tsabar yanda ake tsare komai nata, wai a hakama dan shima wani ne….

 

Anfi minti talatin sannan ya hangota tana tafe cikin takunta me birgewa da gayunnan nata daya santa dashi haryanzu yananan, shi sai yaga kamar ma yarinta ta kara dan bazaka kalleta kace tanada da’ kamar Deen ba, dama familynsu haka suke sunada diri da kyan jiki,….

“Bana bukatar wani permission din shigowa wannan cage din naki da befi a saka kaji aciki ba!”….

 

“Get out of my house now! Or I sue you for bulging into my space without my permission!”..

 

Dariya yayi sosai dan bayajin ze biyemata yau, dan yanada dalili me karfi daya kawoshi…..

 

“Relax Justice Fatima, niba wannan shirmen bane ya kawoni, nazo muyi magana akan Deen ne, I can’t see my only son stranded for the crime he hasn’t committed, ni nasan bashi yayi kisan ba”……

 

“Wannan kuma chan ta matse maka mallam! Who tell you you’re invited? Ba kace ba ruwanka ba? Muje chan mu karata, toh yanzu ma ba ruwanka!”..

 

“Kema fa kinsan I don’t mean that, tayaya zan zuba ido abu ya samu beloved son dina?”….

 

“Son din dana lalata maka tarbiyarsa ne ya zama beloved? Ko kunya bakaji?”…..

 

“Enough of all this Justice Fatima, ki nutsu muyi abunda ya kamata kinga Deen is in danger, and there’s something I want to tell you nasan ze kara baki highlight akan binciken da kikeyi”….

 

“Kayi kadan ka bani information din dazanyi amfani dashi wallahi mallam, so kake kacemin kaine kayi kidnapping dinsa in the first place? To koma bakai bane ka saurari yanda bincike ze hau kanka, so hold your information to yourself, idan nasa aka kama min kai ze maka amfani gurin bayani, now out!!!”…..

 

“Wai ke meyake damun foolish brain dinki ne da bazaki tsaya ki saurari abinda ake fada miki ba? Me kike takama dashi ne? Nawane net worth din naki duka? Da har kike tinanin zaki iya cin galaba akaina da matsayinki a kotu?”…..

 

Batace komai ba ta danna wani abu, in a blink of an eye securities guda ashirin suka zagaye dad kowannensu dauke da bindigu a hannu, kana kallonsu kuma kasan ba karamin karfi sukeji dashi ba……

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button