Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 56

Sponsored links

Driving take a nitse tsabar yanda take cikin nishadi, inta tuna dramar daddy da mama sai taji wani mugun dariya ya kamata, kida ta kunna dan ta kara jin dadin moment din, sai kuma tashiga tinanin yanda zatayi da wannan aure tinda gashi burinta ya cika kafin akai ga yi, yanzu kuma in tace ta fasa daddy ze zargi wani abun, kodai ta bari a daura tace sai ya saketa a ranar?…. Rasa abun kamawa tayi kawai saita banzatar da zancen ta cigaba da nishadinta…….

 

Hanyar school ta dauka tana ayyana irin tests din datayi missing dan ta dade bata shiga school ba, har tabi normal way sai taga mutane sun danyi yawa a hanyar hakan yasan tabi hanyar da baa samun mutane sosai sai jifa jifa…..

 

Saura kadan suyi karo da wata mota data sharo a guje tayi saurin kaucewa, inda Allah ya taimaketa ba gudu takeyi ba, ganin me motar yayi parking yasata fitowa daga tata motar da sauri da niyar ta zazzagawe meshi balaki dan shine ya biyo one way..

 

Fitowa wanda ke cikin motar yayi fuskarsa dauke da mask yana nufota gadan gadan……

 

Bata damu da mask din dayasa ba cikin isa tace;

 

“Kai wani irin mahaukaci ne da baka kallon gabanka sai kace……”

 

Bata karasa ba taji numfashinta na sama sama, batasan meya shaka mata ba saiji tayi komai na jikinta ya tsaya chak lokaci daya…..

 

Cikin sauri ya turata cikin motar gudin kar wani yazo ya gansa, mutane uku dake bayan motar yama alamu dasu fita su shiga tata motar, fita sukayi da sauri shikuma yaja motar a guje……

 

Saida yayi tafiyar kusan minti talatin kafin yayi parking a gaban wani mini apartment da suke kira da ‘base’…..

 

Daukarta ya kuma ya shiga da ita ciki, be direta a ko ina ba sai a daya daga cikin bedrooms din dake parlour….

 

Kallon kyakkyawar fuskarta me daukan hankali yayi yana fadawa kanshi ‘she’s mine’ kome ze faru dole ya sameta, toh mema ze faru when he have her all to himself now? Ai sai abinda yaga damar yi da ita… Koda baze sameta ba gwara ya dana ya rage zafi ballema yanaji a jikinsa saidai khaleel ya hakura ya bar masa kawai idan yagama da ita….

Hand gloves dinta ya cire ya shiga shafa zarazaran yatsunta masu azabar kyau, da palms dinta me laushin gaske, sosai yaji ya fara shiga wani yanayi, wai iya hannu kenan ma? Kokarin cire hijab dinta ya shigayi sai wani tinanin ya fadomasa, ‘shit’ ya fada yana lalubar wayarsa a cikin aljihu…. Yamanta duk wannan plan din Deen be saniba, kuma ya kamata ace yasani tinda shi yake basa shawara, shi sameer sam bega baiken abinda yayi ba, ganin yake kamar yayi abinda ya dace ne……. Sai ya shiga kiran number Deen….

 

Deen na zaune abin duniya ya ishesa ga guilty conscience din da yake damunsa tun bayan yayi barin zance a gaban Umm da mami, kuma har yau basu kara zuwa ba… Gashi an kara masa damuwa akan damuwa na dauketa daga asibiti da akayi, da yana tinanin ya saci hanya yaje ya ganta a hospital yanzu kuma batanan gabadaya, ya kuma rasa wanda ze fadawa damuwarsa yaji dadi, shi haka Allah yayisa da mugun zurfin ciki babu wanda yakejin cikinsa saidai friends dinsa su kawo nasu ya basu shawara koya taimaka musu ayi abinda ya dace, shiyasa kullum suke masa kallon wanda bashi da damuwa basusan na ciki na ciki ba…….

 

Kamar kullum ana kawo masa wayarsa na yan mintina yayi amfani da ita haka yauma ta kasance, saidai ko an kawo baya komai da ita, mami ce kadai ke kiransa dan ita kadai tasan da waya a hannunsa dama kuma ba business line dinsa bane so few mutane ne suka sansa da line din……

 

A irin wannan lokacin yaji wayarsa na ringing, dauko wayar yayi yana tinanin mami ce sai yaga sunan sameer na yawo akan screen din, dauka yayi yana karawa a kunnensa…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button