Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 47

Sponsored links

Wani kallon banza Deen ya masa ya rungume hoton yanda bazasu gani ba yace;

“I didn’t ask for your compliment! I know she’s beautiful!”……

“Wow such a jealous fellow!”….

Harararsa Deen yayi ya tashi ya mika musu atm card dinsa still kirjinsa rungume da hoton yace su cire kudin materials dinsu da yayi using, cewa sukayi ya barshi for the sake of the beautiful design, ai sai suka kara kunnashi yayita bala’i wai mutane basa gani suyi shiru, ya karbi card dinsa ya watsa musu cash din dake aljihunsa kamar ze dake su sannan ya fita, kallon mamaki suka bisa dashi suna tunanin sunyi abun arziki sai gashi abu ya juye musu……….

Tafiya ya cigaba dayi yana rungume da zanen kamar zaa kwace masa, plan dinsa a da shine ya zanata ya dinga nunawa mutane hoton yanda zeyi saurin ganosu, amma yanda yaji wa’enchan suna koda zanen ko sama da kasa zasu hade baze iya kara nunawa kowa ba, haka ya cigaba da yawo yana nemansu da description kamar yanda ya fara, yana cikin wannan hali yaga call din sameer ya shigo wayarsa da number Nigeria dinsa, dake akwai wani clone application da zaka iya cloning number Nigeria dinka data wata kasar sai a kiraka da number Nigeria normal ya shigo, dauka yayi da sauri jikinsa na rawa yace;

“Sameer ya ake ciki? Ya gaya maka inda suke a dubai din?”…..

Daga daya barin sameer yayi wani murmushin mugunta ganin yanda Deen ya wani damu sosai dan shi fa haryanzu be yadda Deen ba, in ba hakaba meye hadinsa da khaleel? Sannan takaicin kin daga wayarsa da khaleel beyiba ya sashi kiran Deen ya shirgasa dan baze zama shi kadai yake suffering ma wulakancin da khaleel ya masa ba bayan yaci burin zuwa ya bata aure…….

A Iran azahar ta masa ya shiga Nasir al-Mulk Mosque yayi sallah, kamar a dubai haka ya zauna ya kwararo addu’a akan Allah yasa ya gansu anan, saidai kash haka ya karaci yawansa kamar yanda yayi a dubai ko alamunsu babu, yanajin yanda kafafuwansa suke masa nauyi amma baze iya hutawa ba, gani yake lokacin daze huta kila lokacin ze gansu, haka yayita zagaye Iran duk sanda yaji kiran sallah ya Parker yayi sallah yayi addu’oi ya cigaba da tafiya kamar me hijira……..

A haka har wata washe garin tayi, wani supermarket yagani kusa da wani hotel ya shiga ya siye kayan da ze chanza sannan ya shiga hotel din yayi wanka ya shirya, shayi kawai yasa aka kawo masa yasha ya dora daga inda ya tsaya ko tinanin bacci bayayi…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button