Hausa Novels and Stories

Auren Wata Tara Complete Hausa Novel

Sponsored links

🅿️………*1 & 2*

 

*FUNTUA*

_Unguwar Jabiri_

 

Tafiya suke cikin unifoam d’in Islamiya su biyu suna tafe suna hira kadan_kadan.

 

Asmy ce ta daddabo Zarah ta ce “Zarah gafa mutumin yau ma ya na kofar gidan Ku kuma wlh nasan ke ya ke jira ”

 

Tsaki wacce aka kira da Zarah taja cikin sanyi murya da daman Chan tun asali haka muryarta take komai takeyi zatayishi cikin nutsuwa da sanyi ta ce .

 

 

 

“Aiko bazan shiga gidan yanzu ba Allah har sai ya tafi ” sai sannan na K’are mata kallo doguwa Ce mai matsakaicin jiki

 

 

Choculate colour Ce bazaka kirata fara Chan ba haka kuma tafi karfin ka kirata da b’aka

 

tana da round face da dogon hancinta sai d’an k’aramun bakinta da ya d’an tsuke ya bada shape d’in heart Dimple d’inta guda biyu dukkaninsu sun lotsa

 

wanda tun asali haka suke ko batayi magana ba a lotse wanda suke k’ara fito mata da ainahin baiwar kyaun da Allah yayi mata Fuskarnan tata fresh ba komai sai kwalli da ta kurtawa idanunta Kad’an

Zarah tana da Bala’in shape Wanda ake kira da shape d’in Coca-Cola diri da Zati da Allah yayi mata shine Babban abunda ke Jan hankalin maza gareta Dan Zarah badai diri ba Dan koya tayi tafiya haka zakaga hips d’inta na Juyawa

 

 

 

Wanda saika d’auka da gangan ta ke yin hakan alhalin itama Ba so take ba danma koda yaushe cikin hijab take amma dukda manyan hijaban da take sanyawa baya hana bayyanar da surar da Allah yayi mata.

 

 

“Kama hannunta Asmy tayi cikin Sauri suka shiga gidansu Wanda madaidaicin gida ne Suna shiga Ajiyar zuciya Zarah ta sauke ta ce ” Allah yasa mayen bai ganmu ba dafa saiya biyo mu ko”

 

 

Aiko da ya biyoki wlh da yaga yanda ake Rashin mutunci Dan ni ba ke bace danfa ya ganki haka salo salo ba umm ba umm umm shiyasa ya rainaki wlh Zarah ki rage sanyin nan Lafiyarki tayi yawa haba ayi mutum kullum cikin sanyi dukda wannan halin naki ya sanya har Rabi take maki irin abunda take maki Dan taga bata gamu da y’ar zamani ba haba ke Ko a makaranta Saidai na shige maki fad’a to tun wuri ma wlh ki koyi kare kanki haba hakurinki yayi yawa wlh ”

 

 

“Asmy ta k’arasa fad’a tana huci “Mamanta ce Da ta fito daga kitchen ta na sauraransu ta ce ” Zarah karki biyeta kici gaba da yanda kike Allah yanason masu hakuri kowani d’an adam yana da nashi kalar jarabawar kinji ke kalar taki kenan kiyi kokari wajen ganin kin cinyeta Allah ya kawo maki sassauci cikin al’amuranki ga abinci nan kuzo Kuci kunji”

 

 

k’asa da kanta Zarah tayi tana Goge hawayen da suka zubo mata na tausayin kanta ta ce “Insha Allahu Mama ” Kallon Asma’u mamanta tayi ta ce “Karfafa mata gwuiwa ya kamata ki dingayi kullum ba Wai Zuga ta ba kinji” gyad’a mata kai asmy ta yi ta ce “Insha Allah Mama ” Tuwon Shinkafar da yaji Miyar taushe mai dadi da Mama ta zubo musu suka zauna Suka fara ci.

Bayan sun gama Ci nan suka fiddo Littafansu na Islamiya suka dinga duddubawa Dan yanzu gaba d’aya hankalinsu ya na Ga saukar da ke tinkarosu Bayan sun gama dibawa jin ana kiran Sallar magriba ya sanyasu tashi Bayan sun gabatar da Sallar magriba Hijab d’inta Zarah ta sanya ta ce Bari na wuce gida sai da safe “Bankwana tayiwa maman asmy tare suka fito su biyu Kasancewar gida Ukku ne tsakaninsu sai nasu Ajiyar zuciya Zarah ta sauke ganin Nura baya nan A daidai bakin k’ofar gidan Asmy ta tsaya ta ce ” Sai Gobe Zarah Zan wuce “Kallonta tayi ta ce ” bazakizo mu shiga tare ba “Girgiza kai Tayi ta ce ” Saidai kawai mun hadu gobe”to Sai Allah ya kaimu kawata ta fad’a ta na kutsa kanta cikin gidan cikin siririyar muryarta tayi sallama a hankali

 

 

k’aramun gida ne d’aki hud’u d’aya na Mama Rabi d’aya na Baba sai na ukkun nata na hudun kuma na.kannanta ” a tsakar gida ta tarar da Mama Rabi tana ganinta ta watso mata wani banzan kallo cikin Masifa ta fara magana da cewa “an fake da Islamiya ana yawon karuwanci Dan matacciyar uwarki Da kikaje kika zauna uban wani zai d’aura miki girkin ne Eh ko kin Aje wani ne a gidan?girgiza kai ta fara tuni harta fara hawaye dan a rayuwarta kome Mama Rabi zatayi mata batajin ciwon shi kamar irin yanda take zagar mata Mahaifiya da ke k’asa Goge hawayenta tayi cikin muryar tsoro ta ce ” Kiyi Hakuri Mama “Tsaki Rabi taja tare da mik’ewa ta ce ” Kafin nan da minti Talatin na baki ki gama yimun tuwo da miya Dan uwarki”to “ta fad’a gabanta na fad’uwa tare da shiga kitchen din.

murhu biyu ta hura dukda iccen jik’e ya ke kasancewar yanayin damuna Haka tayi ta hura wutar cikin k’ank’anin lokaci ta na Sauri ta gama Duka ayyukan tukwana ta fito ta yi wanke wanke Su Habiba na Nan zaune suna latsa waya ba Wanda ko tsinke ya kama mata Harta gama komai tukwana ta wuce d’akinta Dan hutawa Cire kayan jikinta Tayi Tare da daura zani Dan zafi takeji kodan yanayin garin kamar akwai hadari a kasa ya sanya zafin fitowa tayi a lokacin Mama Rabi suna cin tuwo ita da yaranta Tab’e baki tayi tare Jan tsaki ta ce “Sai anje an gama yawon ta bugas din azo ana wankan iskanci a gida ” Idan da sabo ta saba hakan yasa ko a jikinta harta fito daga bandaki Bayan tayi alwalar isha i d’akinta ta wuce tare da shimfida tsohuwar dardumarta ta sanya hijab d’inta ta Islamiya ta kabbara salla

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button