Hausa Novels and Stories

Auren Shehu Hausa Novel Page 4

Sponsored links

Maimakon da ta fito ta yi azama wajen rama sallolin da ake bin ta, wato Asuba da Azahar, sai ma tsayawa ta yi gaban madubi ɗaure da tawul da ya tsaya iya gwiwa, cikin jin daɗi da alfaharin baiwar dirin da Allah ya mata, da ke masha Allah ita kan ta ta san Allah ya mata mata dire. Hakan ya s koda yaushe ta na kan social media cikin saka hotunan ta wanda ta yi da matsattsun kaya, dan kuwa ta na cikin ɗaya daga cikin sannanun matan nan da ake kira “Slay Queen” a Instagram.

Sai da ta ɓata lokaci wajen shafe shafe da kwalliya, ta fito fes cikin ɗinkin atamfa riga da siket, sannan ta ɗauko hijabi wanda ya ke kai mata har ƙasa ta sanya. Murmushi ta ke ganin yanda ta fito saliha sak, ita da kan ta ta shiga yiwa kan ta kirari

“woo ni Zeee the slay mama, the club mama, kuma salihar Daddyn ta”

Nan ta gama juye juye gaban madubi, sannan ta shimfiɗi sallalaya aka shiga jera sallar asuba da azahar.

Malam Abubakar Birma sananne kuma hamshaƙin Malami ne wanda ya yi suna a Nijeriya, musamman Kano da Maiduguri. Babarbare ne ɗan asalin garin Maiduguri. Matan shi biyu, Hajja Kulu ita ce matar shi ta farko, wacce ta ke ƙabilar Barebari, ta na zaune ne gidan Malam da ke birnin Maiduguri. Yaran ta da shida, maza huɗu da mata biyu. Sai kuma Hajja Aleesha, wacce ta ke ƙabilar Shuwa Arab. Ita ce ke zaune Kano, ƴaƴa uku gare ta, kuma duka mata, sun haɗa da ɗiyar ta ta farko Zainab mai kimanin shekara ishirin da biyu, wacce ake kira Yakura, sai mai bi mata, Halitta mai shekara ishirin, sai auta Falmata, wacce ta ke da shekaru goma sha takwas a duniya.

 

 

 

Cikin ƴa’yan Malam, Allah ya jarrabe shi da fitinanniyar ɗiya, wacce babu wanda zai ga ɗabi’un ta ya danganta ta da Malam. Ba kowa ba ce fyace ɗiyar Hajja Aleesha ta farko, wato Zainab. Club ne daga na cikin gida Nigeria kudu da Arewa har zuwa ƙasashen ƙetare babu wanda ba ta zaga ba, sai dai wanda ba ta sami dama ba, haka kuwa buɗe ido babu wanda Zainab ba ta yi ba kasancewar ta na yawan harka da gurɓattun yaran masu kuɗi, yawanci ta haɗu da su ne ta cuɗanyar makarantun boko da su ka yi tare.

Malam Abubakar Birma sananne kuma hamshaƙin Malami ne wanda ya yi suna a Nijeriya, musamman Kano da Maiduguri. Babarbare ne ɗan asalin garin Maiduguri. Matan shi biyu, Hajja Kulu ita ce matar shi ta farko, wacce ta ke ƙabilar Barebari, ta na zaune ne gidan Malam da ke birnin Maiduguri. Yaran ta da shida, maza huɗu da mata biyu. Sai kuma Hajja Aleesha, wacce ta ke ƙabilar Shuwa Arab. Ita ce ke zaune Kano, ƴaƴa uku gare ta, kuma duka mata, sun haɗa da ɗiyar ta ta farko Zainab mai kimanin shekara ishirin da biyu, wacce ake kira Yakura, sai mai bi mata, Halitta mai shekara ishirin, sai auta Falmata, wacce ta ke da shekaru goma sha takwas a duniya.

Cikin ƴa’yan Malam, Allah ya jarrabe shi da fitinanniyar ɗiya, wacce babu wanda zai ga ɗabi’un ta ya danganta ta da Malam. Ba kowa ba ce fyace ɗiyar Hajja Aleesha ta farko, wato Zainab. Club ne daga na cikin gida Nigeria kudu da Arewa har zuwa ƙasashen ƙetare babu wanda ba ta zaga ba, sai dai wanda ba ta sami dama ba, haka kuwa buɗe ido babu wanda Zainab ba ta yi ba kasancewar ta na yawan harka da gurɓattun yaran masu kuɗi, yawanci ta haɗu da su ne ta cuɗanyar makarantun boko da su ka yi tare.

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button