Hausa Novels and Stories

Abban Sojoji Chapter 5

Sponsored links

Fitowa ta yi tana leƙensa, lalla6awa tayi ta ƙaraso gabansa kamar wata munafuka tace “barka da fitowa yaya Junaid,” ɗagowa yayi tare da kallonta ya ce “zan fita masallaci before na dawo pls a shirya min abinci bazan iya jurewa ba cos am starving,” dariya ce ta kusa kubce mata hannu tasa a bakinta, harara ya jefa mata “dariyar uban me ka ke?

hannun ta cire daga bakinta tare da cewa “dama….ran nan ka ce min baka iya cin abinci saboda tare da brothers ɗinka kke ce kun sa6a dole sai kun haɗu sannan kke ci atare shine….” tsayawa ta ɗan yi tana kallonsa

 

sakin baki yayi yana kallon wannan ɗan rainin hankalin ɗan aikin nasu, rai abace ya ce “kai !! NI tsaran wasanka ne ? raini ya fara shiga tsakanin mu ko !” ya ƙarasa maganar yana kallon ta,

 

Hankalin ta ba ƙaramin tashi tayi ba, bakin ta ya ja mata,

 

Saboda bacin rai muryarsa har rawa yake yi wurin kwalawa azmi kira,

Nan fa ta aza kai a saman ka tana faɗin “wayyo Allah na Sorry sir,”

 

duk a tunanin ta korarta zai sa ayi, jiki na rawa azmi ta fito baiwar Allah kana ganin ta kaga wadda bacci bai isheta ba,

 

Ƙaraso wa tayi tana faɗin “meya faru junaid kke kwalamin kira,”

 

Mayar da idonsa ya yi akanta ya ce “wannan mai aikin so nake nabasa punishment, cos he distains me ,

 

Ya ƙarasa maganar tare da kallon sehrish ya ce ” kasan yadda ake tsallen kwaɗi ko,” cikin tsoro ta girgiza masa kai alamar bata sani ba,

 

Jinjina kansa yayi tare da cewa “amma kasan yadda ake up and down,”

 

Zuru tayi da ido don batasan me ake nufi da up and down ba, juya wa tayi ta kalli azmi,

 

da ido azmi tayi mata alamar tace masa batasani ba,

 

Amma rashin fahimtar hakan yasa ta ce masa “eh na iya,”

 

cike da bada umarni ya ce “azmi inaso ki samun ido akansa, har nadawo daga masallaci nasame sa yana yi if not kowa zai gane kuransa,”

Yana gama faɗar hakan yasa kai ya fice,

 

Kallonta azmi tayi tana murmushi tace “oya start ae ke kika ce masa kin iya, ke kinsan menene up and down kuwa? mugun punishment ne mai wahalar gaske,”

 

murya na rawa tace” i don’t know how to do it ,”

 

Dariya azmi tayi , tare da gyara tsayuwarta, ta some yin ƙasa da sama tana nuna mata yadda zata yi,

 

“Toh kin ga yadda zaki yi, maza ki fara kafin ya dawo sbd kowani lokaci zai iya faɗowa, ni zan koma ciki saboda haryanzu kaina ciwo ya ke min,”

 

tana gama faɗan haka ta shige ciki, zugudum sehrish tayi ganin ba kowa yasa ta lalla6a tasamu wuri saman 2 seater tazauna, daga taji motsi sai ta ɗan firgita in taga bakowa sai ta natsu,

 

zaman zuru tayi ga fargabar karya zo yasame ta zaune batayi abinda yace ba, bacci ne ya ziyarce da kuma dama kowa yasan bacci 6arawo ne, nan ta soma gyangyaɗi a hankaki yayi Wuuuf da ita,

 

Tsayawa yayi cike da mamaki yana kallon ikon Allah, mutumin da aka ba punishment ya shi baiyi ba, kuma yasamu wuri dirshen kamar ɗan masu gidan ya kwanta,

Jinjina kai junaid yayi wanda shigowarsa kenan, zuwa yayi inda tanƙamemiyar freezer ɗinsu take yasa hannu ya buɗe, robar ruwa ya dauko mai sanyin gaske har ya fara kankara,

 

Yana zuwa inda sehrish take, ta saki baki baiwar Allah sai sharar bacci take yi ga gashin bakin nan da take manna wa yamayar da ita wata yar cartoon guda,

 

Buɗe murfin robar yayin, kai tsare ya zazzage mata shi ajikinta,

 

Wani irin firgit tayi ta farka lokaci guda ta tashi zaune jin yadda ruwa mai sanyin gaske yayi mata dirar mikiya,

dogon numfashi taja tana sa hannayenta tana yarfo da ruwan dake zuba a fuskanta, idonta jawur ta ɗago ta kallesa,

 

faɗa yasamo yi mata” saboda raini in saka ka aiki kazo kasami wuri ka zauna kana bacci ko kai ga riƙeƙƙen ɗan bariki ko,”?

 

Saboda tsananin baƙin ciki fashe mashi tayi da kuka kamar jinjira, tama rasa me zata yi, me zatace masa

 

Ganin yadda tukur ɗin ke shesshekar kuka yasa yaji kamar baiyi adalci ba, kasancewar junaid nada matukar tausayi wani sa’in,

 

juyawa yayi ya mayar da robar ruwa, sannan ya dawo ya zauna kusa da ita, har lokacin kuka take kamar ranta ze fita,

Muryarsa ce ta ratsa sa” Am sorry” ɗagowa tayi cikin mamaki tana kallansa bata ta6a tunanin zai iya bata hakuri ba,

 

Ci gaba da magana ya yi ” ka gane am very simple man kaine ka cika sa ido,komai kaji sai kaja bakin ka kayi shiru karka sake mun haka !,”

 

Tsagaitawa tayi da kukan tace” kayi hkr bazan ƙaraba bazan ƙara ba insha Allah,”

 

yanayin yadda tayi maganar sai ya ji kamar muryar mace amma aduk lokacin da yaji hakan sai kawai yasa wa ransa cewa namiji ne saboda akwai waɗan da halittarsu ce hakan,

 

“Its ok now i need something to it, go get it for me, am waiting ,”!

ya faɗi hakan cikin nuna buƙata, ta shi tayi ta nufi kitchen tana mai tunanin me zata sama masa ya ci, babban tashin hankalin ta azmi bata jin daɗi hakan na nufin cewa yau ita ce zata haɗa masu dinner kenan, gashi bata iya irin girkinsu ba na ƴan gayu,

 

da wannan tunanin ta shiga kitchen ɗin, babu wani dafafen abinci sun cinye komai da safen nan, dole sai dai tayi preparing wani, cikin gaggawa cos he needs it immediately,

 

cikin sauri ta za masa taliya saboda ita ce abu mai saurin dafuwa, kayan miya ta ɗebo ta gyara su ta markaɗesu , ta haɗa da kayan kamshi duka, ta jagwal gwala masa sai gashi ta fara ƙamshi, murmushi tasaki “Allah sarki har miyau na ya gwada bari in zuba masa sai in rage saura nima inci,”

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button