Hausa Novels and Stories

Zafin Kai 18

Sponsored links

Har suka tashi sama sama take dan haka ta riga Benazir komawa gida tana isa gidan dole ta kamawa Anne aiki saidai ko rabi batayiba ta yanke jiki ta fadi Allah yasa Yauma hande bata gidan dan haka Anne cikin firgici ta zuba mata ruwa ta farfado sukai daki ta kwanta.

Koda Benazir ta dawo jikin nata yayi dan tsanani saidai tana bacci dan haka batayi dogon motsiba dan kar ta tadata ta fita suka cigaba da qarasa sauran aikin.

******Bayan kwana biyu sunata jinyarta a boye ba tare da sanin Hande ko Ababa ba,

Tana cikin rashin kuzari ko kadan ga yawan Amai yanzu datakeyi babu wata wata Anne cikin tashin hankali da baa saka masa rana ba tace wlh ciki ne a jikin Sumayyahn.

A zaune suka kwana dare cikin matsanancin tashin hankali da fargaba da jiran tabbatarwa,

 

Daqyar sukaga gari ya waye cikin rashin sanya yau suka tattara sumayyar ta dan samu qwari suka fice makaranta sbd a can zasu samu tabbacin Zargin Annen.

Kaman yanda Benazir ke addua Alh bilal dinne da kansa yazo daukansu ganin halinda Sumayyah take suka wuce kai tsaye asibiti sina zuwa aka kwantar da ita.

Tashin farko likita ta iso musu da sakon ciki ne a jikin Sumayyah na sati hudu.

, Wuta ce ta dauke masa Benazir kuwa duhu idanuwanta sikai lokaci daya kuma qafafunta na kasa daukanta ta zube qasa tana kokarin samun ganinta ya dawo.

 

AFUWAN PLS BA YAWA WLH INADA UZURI YAU

 

Follow me on Arewabooks @Mamuhgee dan samun pages dasuka fi yawa.

 

#MAMUH#

 

#DD KAANTE #BENAZIR ABABA#LITTLE BENA#HOTHOT#LOVE#ROMANCE#ZAFIN KAI#BILLONAIRESromance#sumayyah Ababa.

Ganinta neman gagararta dawowa yayi sbd bata taba samun kanta a mafi tashin hankali irin na wannan daqiqun ba datake cikinsu a yanzu,

Cikin haihuwa fa ake magana sumayyah take dauke dashi,

Ta haifa ‘da ko ‘ya masu rai fa,Innalillahi wainna ilayhi rajiun,

Qalu innalillahi wainna ilayhi rajiun,

Ya ilahi meye haka kunnuwanta yau sukaji,

Babbar kadaddariyar jarabawarsu ce yau ranarta ta tsaya,

Tsikar jikinta ne gabaki daya suka tashi sbd tinaninta daya dade da tsayawa babu abinda take gani sai gawar kansu su uku ita da Annensu da sumayyar harma da cikin.

Bilal kaante kuwa wutar data dauke jikinsa babu abinda yake zuwa kansa sai tausayin Sumayyah da abinda yake cikin wanda baisan me zai fada akansu ba yanzu,

Kalmar cikin ta girgiza sa ne sbd abune da bai taba zuwa tinaninsa ba a wannan lokacin.

Shi kansa a nasa bangaren wannan wani babban qalubalen ne da tashin hankali sbd tsakaninsa da iyayensa da danginsa wani abune da ko zasu rasa komai bazasu yarda da wannan zancenba sbd karma ya fita,dan gwara ya jewa dd babba da dad kaante da labarin sunyi asarar miliyoyin kudi masu yawan da hankali bazai dauka ba akan yaje musu da wannan labarin.

Daga shi har Benazir babu wanda yakeda nutsuwa ko tinanin kallan junansu kowannesu da nisan da yayi cikin nasa tashin hankalin da baa saka masa rana ba.

Kaman masu jiran sakon mutuwa haka suke babu me motsi,har lokacin Benazir na zube qasa zaune batada qarfin tasowa shima har lokacin yana tsaye,

 

Benazir tashin hankalinta yasa tini ta manta da yanayi sumayya tinaninta akan cikin yake har lokacin dan kuwa zancen ya kasa zaunuwa a ranta tayaya sumayyarsu zata samu ciki?

Ina ta samesa?

Da wa?

 

Sam kanta ya kasa daukan zancen bare tasan yanda zuciyarta zata aje zance

Acikin zaman jiran da baifi na awa daya ba Idanuwanta sukai wani fadawa tareda yin jajir

Daqyar take iya hadiye busashen yawu a makoshinta daga bakinta daya bushe qayau,

Bilal kaante kansa bakin nasa a bushen yake saidai yanayinsa yasa baa iya gane zallar damuwa da tashin hankalin dayake ciki.

Sumayyah batasan halinda take ciki da wanda suke ciki sai bayan awa hudu data share tana bacci sbd ruwan bacci dayake cikin ruwan da aka daura mata,

Tana farkawa Abinci mai lafiya da rashin nauyi Bilal yasa aka kawo mata,

Tana farkawa Abinci mai lafiya da rashin nauyi Bilal yasa aka kawo mata,

 

Benazir har lokacin bata dawo cikakken hayyacinta ba gabaki daya bata gane komai sosai dan haka tana gefe rakube tayi zugum batasan me take tinaniba ita kanta tadai san tana cikin mafi girman tashin hankalin rayuwarsu.

Shine da kansa ya bawa sumayyar abinci cikin kulawa da so mai tsanani yanajin inama da aure ne tsakaninsu wannan qaddarar qaruwar ta same su da sai ya nuna mata soyayyar da zata manta da quntatacciyar rayuwarsu ta baya,

Yanzu gashi qaddara ta riga fata,waye zai fara tara da wannan maganar mai girma?

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button