Hausa Novels and Stories

Yar Aikin Karuwai 90

Sponsored links

Juyowa nayi nace Sannu ko,wani Murmushi Papa ya saki suna bala’in Kama da Nawwar,nace wata kwangila dama Zan baka jiya abinda ya kawo Ni kenan Ina son hada harkalla da company dinka, Star ce ta Kira a waya na sata a handsfree nace sister ya akayi ta Wayar tace Zan wuce Uk ne nan da 2hrs kudin da Kika manta a dakina Zan kawo Miki ni nayi shiri na,address na Bata na kashe Wayar,Papa a ransa yace wato har kudi ake iya mantawa a dakin wata lallai kudi ya musu yawa inama Ina da yaro na sa ya nemi Aurenta mu ai min huta,Amma ko ni ai da kuruciyata na aureta mana kawai yanda nake din nan ai dai dai nake da Nawwar, Papa Murmushi ya sakarwa Wise tare da furta me za a kawo Miki to ki sha?nace ba komai,yace a’a Yan Mata ko makoshinki ai kya jika,tace just water ta furta,da Kansa ya tashi ya kawo Mata ruwa Eva,ba a dade ba sai ga Star taci wanka na kirki kamar zata je chasu cikin kana nan Kaya tazo har Office din Papa me kyau,Papa Yana washe baki ko gaisar da shi Star Bata Yi ba tace Eesha ban son shirme me yasa Baki da tarbiyya ne shi yasa nake son Sarah ta fiki hankali ki gaida shi Mana first,Star tana turo baki sis Daddy fa jirana yake ta karasa da shagwaba ga Mummy yau zata wuce Kaduna itama for God sake ki karba na wuce ohh fuck,bani bani please,Papa yayi zuru yace lallai gata ya musu yawa yayan gata ne an tabarasu da kudi,hand bag star ta bude Papa yaga dollars da Bundles na Yan dubu dubu cikin jakar a ransa yace ke dan Allah Ina sonki kai ji kudi, Kawai Wise ta karbi kudade ta maida Jakarta tace wait bari na rakaki airport,Star harda doka kafafu na shagwaba,Wise ta mike tace kayi hakuri yarinya ce please bari naje Zan dawo next tomorrow, Alright… Alright cewar Papa duk ya rude,yace please can i have your number? Wise tace yeah why not ta karanta Masa ya shigar ya Kira tayi saving tasa sannan Suka fice,Suna barin layin a mota Suka tafa Star tace kinga yanda ya rude Kuwa Suka sake tafawa,Sabreen Ina zuwa kwanan nan Zan zama Mamanki.

Kwana biyu Baffa ya hau Kiran Wayar Mami amma tana kallo taki dagawa,gashi bai San Ina zai sameta ba,Sultana da Nasrin sune Suka Zama Iyayen sune suke komai a part dinsu,Baffa ne ya shiga part din,Suka gaida shi yace Ina Mamin ku take? Bamu sani ba bata fada Mana ba munyi munyi da ita taki fada Mana sai dai ka tambayi Yaya Nawwar,kunyar Nawwar yake ji bazai iya tambayarsa ba,Kawayen Mami ya fara bi Daya bayan daya Yana tambaya ko sun San inda take Suka ce basu sani ba,ya dinga bin gidajen Nawwar da ya sani amma ba inda ya ganta,ya dinga nemanta amma bai ganta ba,rasa sukuni yayi ya rasa inda zai sa kansa,Iyamami ya samu a part dinta ya sata a gaba ya dinga rusa kuka shi fa matarsa a dawo Masa da ita dake komai girman da a gaban iyayensa to yaro ne,Iyamami tace Kai baka ji kunya ba dan Allah to ka sani aurenku ya Kare bata da sauran igiya taka ,sai tayi aure ta fito,Ni bana so kowa ya aurar min matata,ai sai kayi Kuma cewar Iyamami,yace ai dama nasan bakya kaunata da Yusuf ne ai da kin saurare shi Amma Ni bakya kaunata,

Iyamami baki ta bude tace Sulaiman yaro kake so ka dawo ne hala? Nidai bakya so na wlh a dawo min da matata ko na talauce na daina Neman kudi ai kunfi kowa Jin dadin kudin idan ban daina zuwa Aiki ba Allah ya tsine min,dariya ta Kama Iyamami,ya kalleta idonsa jajir yace Indai matata bata dawo ba in Zama talaka ya mike a fusace ya bar part din,Iya Mami tace ikon Allah lallai shegiyar ta mako Masa asiri tab zata ci ubanta kuwa,baza ta taba dawo Mana gida ba Indai Ina raye ayi mace Kamar ba jinin mu ba.

Mairo Kuwa tana Isa Tasha sai Kaduna a can ta sauka tana tafiya a tashar gab da fita wata matashiya tazo ta bangajeta ta wuce,Mairo ta fisgo rigar Yarinyar nan,tana juyowa ta kantsame Mairo da Mari,Mairo baki ta bude tana zaro idanunawa tace na shiga Uku Rabi kece haka ta ya Kika dawo talaka haka Ina mijin naki ke da Kika goge Kika waye,Budurwar Mai Kama da Rabi sak ba babanci sai dai wannan da alama ba a cikin daula take ba,tace ke uwar wace Rabi din kina lalata min suna Ina Rufaida ki dinga ce min Rabi shegen hancinki Kamar Alkaki ta ja tsaki tace ke wallahi bana Jin magana takadariya ce ni naci ubanki yanzu Yar Kauye chus dake bigi bagiro,wani tsoho ne ya karaso wajen me Kama da Rabi sak yace Cele a kasko kin San tafiyar nan ance Saura wata uku,Budurwar tace ai Kamar yaune Kaka Haba ka isheni ni Ina zuwa kasar Sai siyar da awarata acan ma Sai na Zama Cele a kasko sana’ar da zanyi kenan a kasar, mu tara kudi maganin bala’in duniya,kudi maganin uban kowa,kudi maganin jarabar duniya,Kudi maganin duk wani matsiyaci da matsiyaciya burina Kaka na siyi Skoota Vespa na dinga ja a kasar dama tawa ta tsufa,Mairo tayi galala tana kallo lallai ba Rabi bace,tana kallo Yarinyar ta nufi wata tsohuwar Skoota Vespa ta tsufa tukuf ta haye dogon wandonta ya bayyana na cikin doguwar rigar atamfarta kadaddiya,tsohon ya haye bayanta ta Mata key ta haye abarta tayo Kan Mairo tana Danna Mata ashar tace matsa Dan burar….goyon kaka ce ni ba hankali gareni ba yanzu nayi ciki dake,Mairo ta matsa da sauri ta ja baya,suna wucewa tabi bayansu taga sun hau main road Yarinyar nan da tace sunanta Rufaida harda ihu a titi tana ta zagin masu motoci,mayafinta ya Fadi iskar babbar mota ta dauke shi ta dinga zagin motar nan Kamar Allah ya Aiko ta,tsohon yace tsaya ki dakko mayafin mana kyale banza Kaka ai ya Fadi kenan yaje,Babu fa dankwali a kanki Cele,duk fadan da nake Miki bakya ji taki kulashi a Haka Suka bacewa Mairo,Mairo ta dafe kirji tace kaga Yar guguwa Anya wannan ba yar uwar Rabi ce ba Kuwa cab.

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button