Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 8

Sponsored links

Kamar yanda ya fada haka suka sata a school da islamiyya, suka kuma kaita shopping yace ta dauki duk abinda take so, kasa dauka tayi sai momma ce ta saki jiki ta dinga jidar mata abubuwa kamar gaske….

Hatta drivern da ze dinga kaita school saidai daddy ya daukar mata daban dan be hadata school daya da ya’yansa da suke boarding ba saboda yasan halin mama yanzu zata tada fitina akan hakan, sai ya bawa drivern kudi yace yana bata kullum idan ya kaita school, be bawa momma ba saboda hali irin na zuciya kartasa mata sake saken yana yiwa yarinyar hidima da yawa…..

 

A washe gari kuma urgent tafiya ta taso masa, dole yabar kasar ba shiri bayan ya tabbatar ya mata providing komai…….

 

A kuma lokacin fatima zainab tagane shayi ruwa ne a gurin momma, da farko kitchen ta maida mata gurin kwanciyarta, haka zatace taje ta kwanta ba shinfida ba komai tsabar mugunta, na biyu abinci sai taga dama take bata abinci a rana so daya, wataran in bataci saa bama bata bata, sannan zagi da cin mutunci ya biyo baya, bata sata koda dauke tsinke ne wai karta koya mata abubuwa ta moru a gidan mijin, gwara duk wanda ya kwasa ya sakota dan babu wanda ze yarda ya zauna da wacce ko shara bata iya ba……

 

A lokacin fatima zainab ta kara kulla aminta da codeine shiyasa duk abinda momma take baya damunta, kudin da daddy yasa ake bata kullum akan siyan codeine yake karewa kamar wacce aka yiwa baki, data siya abinci taci ta gwammace ta siya codeine tayita sha, tana sane da cewa smokers and drinkers are liable to die young amma she doesn’t care anymore dan tayi nisan da bata jin kira, abun nata har ya wuce addiction ya zama disorder…..

A gurin abdul kanin khaleel kadai take samun sauki saidai shi ba mazauni bane dan a boarding school yake shima, sosai yake shiga damuwa akan yanda take inactive koda yaushe, wani zubin yana mata magana batasan me yake cewa ba, haka zatayi ta bashi unrelated answers, tun yana karyata zuciyarsa harya fara zargin shayeshaye take saidai binciken duniya ya kasa gane abinda takesha cuz she knows how to play her game, gashi be isa ya kulata a gaban momma ba dan yanzu zata hau masa fada ta inda take shiga batanan take fita ba, momma ma nasane da shayeshaye takeyi tinda ko a ranar datazo gidan a bige tazo saidai ko a kasan slippers dinta, inma duniyar duka zata shanye bata damu ba……

Mama da aka ware gefe tana sane da muguntar da momma take ganawa yarinyar, sannan kuma ta mata daidai bakincikin ta daya yanda taga momma na wani faffadi akan lamarin yarinyar tana nunawa alhaji tana kula da ita, shikuma sai yayita jin dadi yana mata kyauta yana ji da ita…..

Takaici ne ya isheta ta fara shirya yanda zata tonawa momma asiri har tasamu yarinyar ta dawo hannunta itama ta dandana mata kalan nata azabar batareda daddy da momma din sunsani ba…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button