Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 55

Sponsored links

“Wai ke meyake damun foolish brain dinki ne da bazaki tsaya ki saurari abinda ake fada miki ba? Me kike takama dashi ne? Nawane net worth din naki duka? Da har kike tinanin zaki iya cin galaba akaina da matsayinki a kotu?”…..

 

Batace komai ba ta danna wani abu, in a blink of an eye securities guda ashirin suka zagaye dad kowannensu dauke da bindigu a hannu, kana kallonsu kuma kasan ba karamin karfi sukeji dashi ba……

 

“Before I count five leave this parlor or they get you out! 1……. 2…… 3……..”

 

Dad ya fita da sauri badan baze iya tsayawa yaga abinda zasuyi ba tinda shima yana tafe da nasa bodyguards din, yasan kuma ba karamin hargitsa gidan zasuyi ba, sai a kashe wani garin haka ma, saidan sulhu yake nema a gurinta, so yake su hada hannu akan case din amma taurin kanta ya hanata ta nitsu suyi magana….

 

Tsaki taja ta koma main part dinta, working room dinta ta nufa straightly tashiga typing termination letter, saida ta duba cctv taga duka securities din dake bakin gate din a lokacin da dad ya shigo sannan ta saka sunayensu duka a letter din, bayan ta gama tayi printing out ta fito dauke da letter din a hannu..

 

Karo suka kusayi da Umm daketa nemanta har letter din ya subuce a hannunta, da sauri Umm ta tsuguna ta dauko mata, har zata mika mata sai kuma taga heading din, fasa mika mata tayi ta shiga karanta content din mami na tsaye tana jiranta ta gama ta bata, saida Umm ta gama karantawa tsap sannan tace;

“Why’re you firing them?”….

“They let an idiot into my house!”

“Ikon Allah, waye idiot kuma?”

“Waye banda so called father din Saifuddeen!”….

Dariya Umm tayi tace;

“Au shine idiot din, lallai ma mami, to ai nina basu permission din shigo dashi, kinsan muryarmu daya they probably thought kece,kinga wannan firing letter din bari na yageta ni ya kamata a kora basu ba”…….

 

Harara mami ta aika mata tana fadin;

 

“Sunci sa’a wallahi, ke kuma saiki bari mutum ya shigo baki tambayeni ba?”…..

“Ya zanyi in tambayeki kamar wani wanda bansani bane ze shigo, kudai haryanzu kun kasa dena ga macijinnan naku ko?”….

Bata kulata ba tace;

“Next time karki sakemin haka pls!”..

“Yes ma’am, yanzu ya kukayi dashi toh?”…

” I sent him away! Tsabar renin hankali wai yazo mu hada hannu akan case din bayan yagama cewa insan yanda zanyi a station”…..

“Toh Allah ya kyauta, I already have two suspects according to my investigation!”….

“Wow! weldone barrister, Who are they?”….

“I’ll let you know tomorrow, there’s something I’m compiling for now”…

“No issues”….

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button