Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 60

Sponsored links

Saidai inaa dad be chanja zani ba dukda yayi kokarin ganin yayi hakan amma kamar zugashi ake sai yaji ya kasa, haka mami ta sake jurewa na tsawon wani shekarar lokacin deen na sha uku ya kuma fara gane akwai sabani sosai tsakanin iyayensa……….

 

Wata rana mami taje gida dad yazo daukarsu mami bata fito ba ya shigo ya tasata a gaba su tafi, baffa ne ya fito daga part dinshi ze fita yaji irin munanan kalaman da dad ke jefar mom dashi, yi yayi kamar bejiba ya wuce, daga sama kawai dad yaji sammaci daga kotu washegari, shi da mami suka shirya suka tafi, suna zuwa suka tarar da baffa da mahaifiyar su mami a kotu suna zaune, a take aka sake tambayar mami abinda yake faruwa ta fada bata boye komai ba, aka tambayi dad shima ya tabbatar da hakan amma ya nemi a masa afuwa, nan iyayen mami sukace basusan zancen ba itama mami tace wallahi saiya saketa dama ta gaji, dad naji na gani badan ransa yazo ba ya mata saki daya yana kuka, tin a gurin baffa ya masa kashedi akan karya sake ya tako masa gidansa biko dan shi kuma ga dan shi chan yaje ya rike tinda ba yaro bane, haka suka tafi suka barsa a gurin yanaji kamar yayi hauka….

 

Mom bata taba farin ciki ba irin na ranar dukda ta nuna alhininta a fili saidai sam ba haka take a ranta ba, har wani dan celebration suka hada ita da sabuwar kawarta suka sha shagali abunsu……..

 

Bayan wata daya da sakin mom ta sake komawa gurin bokanta aka mata aiki akan mjinta da kuma dad, tin a ranar ta fara ganin aikin kuwa dan tana dawowa mahaifin hameeda ya bata takardarta, washegari tana tashi kuma taga missed call din dad….…

 

Nan tarayyarsu ta samo asali, dad ya rikice yace sai ita kodan ya rama abinda mami ta masa, ace ya kamata tana zina da wani a gadon aurensu amma ita zatace sai ya saketa bayan shida aka zalinta ya yarda ze zauna da ita a haka, da kyar ya daure ta gama idda sannan aka daura musu aure suka tare cike da begen juna, mami was so heartbroken da taji labarin auren Umm ce ta dinga tausarta akan kartace mata komai kawai ta rabu da ita kowa yayi da kyau zega da kyau sannan tayi kokarin gani mami da dad sun sasanta ana mutunci koda ba aure amma suka nuna mata basa so, haka mami ta rabu dasu tayi focusing on building kanta baffa kuma yayi supporting dinta sosai har ta kai matsayin da take kai a yau, maganar aure kuma tace ta shafeshi a babin rayuwarta………

 

Da farko deen yaso ya bawa mom matsala saboda yanada wayan da yake ganin bata kyauta ba na auren mahaifinsa a matsayinta na aminiyar mahaifiyarsa, sawa tayi shima a mayar dashi sai yanda tayi dashi, be koma yanda take so ba saidai ya zama kamar wani psychopath be damu da kowa ba har iyayensa, harkar gabansa kawai yake, shigowar fatima zainab rayuwarsa ne yasa ya fara sanin damuwa, kasancewar be saba ba yasa besan yanda ake bin abu a hankali ba shidai burinsa kawai ya illata duk wanda ya masa abu, sannan yafi rashin kula mami ma saboda lokacin ta bar abuja gashi dad yace karta sake ta kara tako masa gida bisa ga umarnin mom, ita kuma tayi hakane saboda sharadin da boka ya bata idan suka hadu su duka hudun ma’ana mami dad deen da ita toh asirin ya karye kuma zata haukace, amma dake rana dubu ta barawo rana daya tak ta mai kaya sai gashi ta manta ta biyo dad ko tinanin zasu iya haduwa gabadaya batayi ba…….

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button