Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 32

Sponsored links

“Anything for you my baby, yanzu bari na kira alhaji na fadamasa a fasa daura auren dama sai one zaa daura……

 

Tana katse wayar ta kira dad, bata sha wahala ba gurin hana auren kasancewarta mutum me siyasa da iya magana, haka ta gilla masa karya shi kuma ya hau ya zauna nan taron daurin aure ya watse…….

 

Hamida ko tinda mom ta kashe wayar ta fara tinanin wanda yace a daura auren, bata kawo mom bace saboda tasan mom bazatayi wannan shirin batareda ta sani ba, ‘Yaya Deen’ zuciyarta ta bata akan shi yace a daura auren tinda dole saiya amince kafin ayi, toh ko ya fara sonta ne? Kai amma da taji dadi, dialing numbershi tayi taji a kashe, haka tayita trying duka nambobinsa da take dashi har Allah yasa daya ya fara ringing amma be dauka ba, bata hakura ba ta cigaba da kira still aka ki dauka, wata zuciyar ce tace mata kila kunyar daukan wayarta yake tinda yayi abun kunya yace a daura musu aure, wanka ta tashi tayi da niyar taje gidan wata kawarta ta kirashi da number kawarta maybe nata ne bayaso ya daga……

Luckily tana kiranshi da number friend dinta ya daga means ita yake ignoring, a daidai lokacin kiran waya ya ishe Deen dake nannauyen bacci ya dauka kawai yasa a speaker……

“Ashe haka ka matsu ayi aurenmu shine harda cewa a daura aure baayi biki ba, ashe dai kana sona hhhh, toh wallahi bazan yarda a wani daura aure ba biki ba kuma……”

 

“Shut up you fool!”….

 

Deen ya katseta da wani mugun tsawa kamar ze fasa wayar……

 

“Wake up from your never happening dream, ni zaki yiwa rashin kunya dan ubanki! Toh bari kiji wallahi ko a kafa aka dauramin ke saina kunce na yar, kuma ko mata sun kare a duniyarnan ba abinda zanyi dake dan ban taba kallonki a matsayin mace ba, kije ki gayawa uwarki nace kullin datayi be dauru ba, idan sun shirya mai dake kamar bazawara su daura aurennan, idan kika kara kiran wayata I won’t hesitate to come over, in babballaki sannan na dawo idiot!”…….

 

Wani kuka me ciwo Hamida ta saki bayan ya kashe wayarsa, sosai maganganunsa suka mata zafi harda ce mata kullin da uwarta tayi be dauru ba, toh me yake nufi, tana kuka ta sake dialing number mom ta fadamata yanda sukayi da Deen……

Shiko Deen baccinsa ya cigaba dayi cikin kwanciyar hankali…….

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button