Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 31

Sponsored links

“Ki zo ki bude kofarnan kona ballata! Yau sai kin gayamin wa da wa kika taba runguma a rayuwarki,Ki bude nace!”…….

Banza ta mishi kamar bata jishi ba, haka ya karaci bugunsa bata bude ba, karshe barin part din yayi gabadaya ya tafi yayiwa kansa allurar bacci ko zai samu saukin abinda yakeji, nan take bacci me nauyi ya daukesa………

“Gani nake gwara mu mata aure tinda tanada wanda takeso, har suna batun guduwa kinji”……

“Bazaiyiwu a mata aure yanzu mami, kinga fa bata iya komai na mata ba, shi kuma namiji bashi da tabbas gajiya zeyi da ita da sunyi kwana biyu, gwara a fara koya mata komai tayi aurenta a cikakkiyar mace”……….

“Hakane kuma gsky”….

“Toh kingani, ni wai da in tafi da ita UK tinda na kusa komawa, in bata duk wata tarbiyyar data dace da duk wani abu daya kamata ta iya”……

“This is a nice idea, kinga zata nitsu musamman in taga me takura mata bayanan”…..

“That’s the point!”…..

“Amma bakya ganin ze iya cewa ze biku? Naga kamar ya hakura da aikinsa yanzu”……

“Ah haba shi ya isa ya bimu, sai in tafi da ita a boye toh”…..

“Hhhhh har kin ban dariya, zamu san yanda zamuyi Insha Allah”…..

“Allah ya yadda”…….

Tsaki taja ta dan yaye bargon data rufe jikinta dashi tana tsinema wanda ke kiranta a waya by this time da take jin dadin baccinta, saka wayar a kunne tayi cikin magagin bacci tace;

“Eh mana aurenku, your dream will finally come through shiyasa naketa cemiki ki kwantar da hankalinki baki da miji sai Deen”……..

“This is not the agreement we made, ya zaayi a daura mana aure kamar a kauye, ba event ba komai sai daurin aure?”…….

“No my dear, auren zaa fara daurawa sai ayi bikin afterwards sannan ku tare”……

“Gaskiya ni bazan yarda ba mom, so kike friends dina sumin dariya? Kinsan yanda nagama tsara bikina kuwa? Nida nakeso ayi bikin da baa tabayi a Nigeria ba, atleast muyi weeks ana events sai kice a fara daura aure bayan kinsan yaya Deen baze yarda ayi wani event ba muddin aka daura auren!”……

“Ni na miki alkawarin ba zaki tare ba sai anyi komai daya dace, ina sane da dream wedding dinki and I’ll fulfill that, so nake kawai a daura auren hankalin kowa zefi kwanciya”…….

“Ni gaskiya bazan yarda ba wallahi, abinda in one month time zan dawo, basai a jira na dawo sai ayi gabadaya ba”……

Sai kuma ta fashe da kuka dan babu abinda mom zata gayamata ta yarda Deen ze bari ayi event bayan daurin aure, halinshi ne babu wanda bata sani ba…..

“Ya isa, ya isa, ba zaa daura auren ba sai kin dawo”……

Mom da zuciyarta ta karye akan kukan da hamida takeyi dan ba karamin sonta take ba ta fada…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button