Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 16

Sponsored links

Sai da aka kai ruwa aka kai rana kafin daddy ya yarda momma ta dawo gidan da sharuda dayawa…

 

Haka mama tayita gana mata azaba kala kala hartakai ss2, a lokacin jikinta ya kara fitowa gata da wani kyau na ban mamaki, kowa ita kowa ita, in dai ta sake ta fita sai ance fiyeda mutum goma na sallama da ita kuma duka ya’yan manya kasancewar unguwar ta manyan mutane, sosai abun ya fara damun daddy dan shi burinsa ta samu ilimi me inganci gashi sai hari ake kawo mata, sai yasata ta dena fita sai fitar ta zama dole har lokacin kuma besan da wahalar datake sha a gurin mama ba, abu daya yasani in tazo part dinshi ya mata tayin abinci sai taki ci saidai kayan fruits, daga baya sai yace kullum tana zuwa tanasha tinda tanaso…..

 

A lokacin data kai ss3 sai abun yaci uban nada dan babu lafiyayyen namijin da zai kalleta ya dauke kai, wani mugun farin jini ne da ita naban mamaki, harda marasa kunyan abokan daddy wai sunaso, saida ya taka musu birki sannan ya samu sa’ida….

 

Kyakkyawace sosai son kowa kin wanda ya rasa dan karyar mutum ya kalleta ya kushe duk hassadarsa kuwa, fara ce kal irin farinnan me shegen daukan ido, fatarta kamar ka taba jini ya fito tsabar yanda take sheki toh ba aikin fari balle baki what do you expect?, fararen idanune da ita masu maiko da daukan ido idon ta waresu, saida shayeshayen da takeyi yasa idonta na dadewa bedawo daidai ba, kullum sai kaga idon yayi wani kala shiyasa koda yaushe idanunta a lumshe suke gudun kar a gane halin da take ciki, pointed nose ne da ita me kyau irin wanda daga nisa sosai kana iya hango karan hancin mutum kadama azo maganar kwanceccen gashin girarta dayake baki wuluk da in mutum be santa ba saiya dauka tint tayi , bare reddish soft pouted lips dinta dayake hargitsa lafiyayyen namiji shiyasa kowa ni kare da doki sai yace yanaso saboda jikinta suke bi badan Allah ba, gashi ko yayan mama sun aske mata shi yafi sau goma saboda bakin ciki amma nan da nan sai ya fito yafi nada yawa, wani kalan silky hair ne da ita me tsawo da cika gashi har tsakiyar bayanta, sosai jikinta yakeda laushi dan kwata kwata batasan wahalar aiki ba, gatadai mace har mace amma a zahirin gaskiya muna macece dan ko rike tsintsiya bata iya ba, a takaice dai bata iya komai na mata ba…….

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button