Hausa Novels and Stories

Zafin Kai 5

Sponsored links

Haka suka sake kwana da Anne a hakan babu sauki ko kadan saima galabaituwar datayi ga daurin da sukayi mata yana cin

hannuwanta da qafafunta dole suna kallo sbd ba yanda suka iya,

Sumayyah ce ta fara fahimtar Yanda duk suka bar Annen da safnah a daki sai jikin Annen ya tsananta musamman fizge fizgenta gashi duk ta goge gefen fuskarta har jini yakeyi sbd yanda take goga fuskar daga kwancen datake tana buga kanta.

Cikin mamaki da kasa gasgatawa suka tambayeta meyake faruwa duk suka bar anne tareda ita

Cikin firgita sumayyah tafara hawaye tana riqo safnah din tace “ me kika yiwa Mahaifiyar data haifeki?

Benazir fararen idanuwanta dasukai laushi da galabaita ta zubawa Anne dake sake goge fuskarta da qasa batareda da jin zafin ciwon data yiwa fuskartata ba,

Sarewa qafafuwanta sukayi tanajin kaman zata gaza,

Itama taya qwaqwalwar jin tayi kaman zata buga dan lamarinsu na gab da qarasa tabarbarewa idan suka fara samun son kai da rashin tausayin juna a tsakaninsu.

Safnah da zuciyarta tafara bushewa ta kallesu tasake tabbatar musu da guduwa zatayi ta zabi bin duniya akan zama karkashin Ababa.

Sumayyah kuka kawai takeyi tana kokarin dawo da tinanin safnah din a hanya amma sam safnah taki sauraranta sai hayaniya taso barkewa tsakaninsu

 

Benazir data rasa abin fada ko yi sai kawai ta qarasa gurin Anne ta dagota zaune ta kwantar da kanta a jikinta tana goge mata jinin fuskarya da hannun zumbuleliyar doguwar rigar gwanjon dake jikinta sbd sune suturarsu.

 

Rintse idanuwa Benazir tayi tareda yiwa safnah din kallo daya wadda ke kallonta itama kaman suna yiwa juna kallon dayake faduwar da gabansu su duka biyun saidai kowannensu ya kasa furta kalma ko daya.

 

Daga hakan dakin ya dauki shiru sai hawayen sumayyah dake zuba tana fidda karamin sautin kuka.

Da daddare duk fada da yada maganganun Hande akan rashin fitowar Anne basu ce komaiba sbd kada ta tsananta tace sai Annen ta fito.

Safnah bata saduda ba cikin kwana biyu ta tabbatarda ta zaburar da ciwon Anne gabaki daya ta hanyar dawo mata da yanda Samirah ta rasu da yanda itama zata tafi ta barta,

A ranar da sukai kwana biyar a wannan halin da rana tsaka Suna can suna aikin wankin kayan Ababa dana Hande ga aikin wankin fatar da aka kawo kusan mota biyu sunata yi cikin gajiya da yunwa.

Safnah silalewa tayi ta koma dakin dasuka rufe Annen ta tsaya a kanta tana kallonta tsawon mintina kafin ta sauke numfashi mai zafi ta durkusa ta warware mata daurin da sukai mata na hannuwa dana kafa.

 

Sanin da rana Ababa baya gida Hande ce take tsaronsu ko ina bata zuwa sbd su din haka koma ta fita tabar musu gidan a bude Annensu bazata taba iya guduwa tabar gidanba sbd aikin da Ababan yayi mata daga ranar daya aureta duk tsanani da azaba bazata iya tafiyaba har sai ranar daya gaji yace ta tafi da kansa.

Safnah dataji wani nannauyan abu ya fada daga kan kirjinta bayan ficewar hande fitowa tayi daga mabiyarta ta mufi kofar gidan batareda ko so daya ta waiwaya ta kalli inda mahaifiyarta ta fadi qasaba tana buga kanta sa qasa ta fice daga gidan ta bi ta bayan da Baa nan Hande takeba ta lullube kanta ruf da qaton mayafin Hande data dauka a igiyar shanya ta dosa daji kai tsaye sbd idan ta nufi cikin gari zata dade bata bar garin ba.

 

 

 

Su Benazir dake galabaice suna aiki ba wani qwari ko cikakken kuzari a jikinsu sukaji ihun kiran da Hande ke musu ta katangar bayan gidan da sauri suka taso hankalinsu tashe.

 

Dakin tabi da kallo bataga safnah din ba qarin sautin kukan Benazir ya tabbatar mata da safnah ta tafiyarta kuma tabbas itace ta warware Anne ta sakota,

Kenan da mahaifiyarsu tayi amfani dan cimma burinta a mafi wulaqancin hanya tayi amfani da uwar data haifeta.

Silalewa itama tayi qasa ta fasa kuka mara sauti dan batada karfin yin me sautin ma koda taso.

 

 

 

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button