Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 67

Sponsored links

“Idan zaka fadamin gaskiyar abinda ya faru na kumayi bincike na tabbatar gaskiya ne, I’m assuring you that abinda ze sameka”…

Da sauri cikin kuka yace;

“Wallahi zan fadamiki, bazan yi karya ba”…

“Good, now tell me how you got here, in full details!”…..

Nan ya shiga basu labarin yanda wani ya hadasa da sameer, da irin matsalolin rayuwar da suke ciki, da rashin lafiyar mahaifiyarsa wanda shine main abunda yayi pushing dinsa ya karbi offer din, da irin alkawarikan da sameer ya masa idan ya gama aikin, har zuwa yanda aka barsu sukazo inda Deen yake, sukashi anan su kuma suka fita……

Kamar hadin baki Umm da Mami suka sauke numfashi dan harga Allah sunji tausayinsa saida as an interrogator bazaka gane hakan ba akan fuskar Umm…….

“For how long sukace zakayi replacing dinsa”

Umm ta fada with a serious look…

“For two days sunce maximum three”…

“Ohk ina suka ce zasuje?”.

“Basu fadamin ba wallahi”…

“Da kuka shigo bakaji sunyi wani magana ba kafin su fita?”…

“Akan wata naji suna magana, kamar gurinta suka tafi”…

“Wata?!”…..

Mami tayi interrupting tsabar mamaki…

“Didn’t you over heard their conversation akan location din wacce zasuje”…

Umm ta cigaba da tambaya

Cikin rawar baki da tsoron da har lokacin be fita ransa ba yace;

“Banji ba gaskiya, kamar dai budurwan dayan ce, wanda yake gurin nan kamar rakasa yayi”….

Tafi kai Umm tayi tana kallon mami tace;

“Shit! Kinsan Allah yaya haka kawai naji hankalina be kwanta da visiting din da kikace abokinsa ya kawo masa ba, see the way they fooled us dan Allah!”…..

“They fooled us absolutely, amma karki damu we’ll get them soon, sai sun gane shayi ruwane, I’ll make sure I deal with them mercilessly! Sameer ya bani mamaki, ina masa kallan nittsatse kamar yafi Saifuddeen hankali ashe duk kanwar jace?”….

Mami ta fada cike da takaici….

“Ai ko ni this time around bazan ragawa Saif ba, he’ll see the very other side of me!!”…

Umm ta fada tana daukan mask din data fuzge a fuskarsa, mika masa tayi tace;

“Wear dan in wani ya ganka a haka you’re in big trouble! Wait kasan nature of crime dinsa ma kuwa?”….

Girgiza kai yayi alamun be sani ba

“Ah lallai your dumbness isn’t in this world, how could jump into a job like this without asking for the person’s crime? Imagine a hada baki da yan gurin nan azo a kashesa anan inda kake do you think they’ll give you the chance to claim yourself”….

Cikin kuka ya shiga kada kai dan ba karamin ahigarsa maganarta tayi ba….

“Toh an kashe banza dan shi bashi da asara and I’m very sure ko addu’a bazena maka ba dan mantawa zeyi da kai, hankali kwance ya cigaba da rayuwarsa, so don’t ever try this stupid act okay?”..

“Nasan inda zamu samesa, muje!!!”…..

Saida yayi nisa sosai sannan ya rage gudun daya keyi, tuki yakeyi cikin nitsuwa minti minti yana dagowa ya kalleta yana examining dinta, har lokacin karatun qur’ani na tashi a motar……

Daidai wani katon mansion ya tsaya, horn yayi akazo aka bude masa ya shiga da sauri……

Fadan irin kyawun gidan bata lokaci, duk yanda zaa siffanta gidan baze fadu ba, ba karamin achievement bane ace at his young age yanada mansion kamar haka dako government house albarka, wani in aka fadamasa gidan mallakin Deen ne baze yarda ba….

Parking yayi ya fito da ita a hankali yana dagawa me gadi hannun alamun ya dakata basai ya karaso sun gaisa ba……..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button