Hausa Novels Complete Documents

Abban Sojoji Chapter 8

Sponsored links

“Yeah but we are not sure, ba tabbacin cewa gobe zasu dawo, muna zuba ido dai,’ kanal yusif ne ya bashi amsa,

Jinjina kai captain najeeb yayi tare da cewa “aiko bazan kwana ba, yau zan koma lagos, ba dani ba

 

dariya su kayi hajiya azeema tace “ashe muna da manyan baƙi, lion da tiger zasu dawo kenan, wannan karan bansan da wata rigima zai zo ba, Allah kaɗai yasan jinin da za’a zubar,’

Hankalisu twins ba ƙaramin tashi yayi ba dama suna zaune matse da juna, sunyi zuru zuru, zuciyoyi na bugawa,

Basu kaɗai ba hada fawan da su jabeer da irfan da sauran atakure suke jin kansu, a wurinsu zuwan Babban yayansu ba alheri bane, bawai don basu son shi ba, sai don tsoran abunda zai faru zuwansa,

 

“ae na jima ina bama ishaq shawara akan ya tunzura Abba, ya aurar dasu, wlh indai su kaji mace atare dasu zasu samu weakness ajikinsu su daina jin kansu tamkar dodonni,’ sakin baki su kayi jin abunda aunty babba tace,

 

Azeema tace “da alama bakisan wanene RAFAYET ba, ai rafayet zuciyarsa tamkar dutse take ! ban ta6a ganin mutumin da mace sam bata gabansa ba irinsa, sam bai da shauqi akan mata, ke shi fa hasalima yadda yake kallon jinsin sa namiji haka yake kallon mace,’ 😧

 

ta ƙarasa maganar tana kurbar lemun hannunta, general ishaq yace “kwara ki faɗa mata da kanki may be she will understand it now, i had been explaining to her about rafayet but taƙi fahimta,’ ya ƙare maganar yana kallonta,

Murmshi azeema tayi tare da gyara zama tace “Anzo inda nafi auki, anzo dai dai wurin ba mai sauka, rafayet da kike gani ba mutun bane ……..

 

dariya ce ta kubce mata su kansu dariyar suke ba don komai ba sai don maganarta takarshe da tace rafayet ba mutun bane,

dakyar ta saita dariyar ta ci gaba da cewa, ” Ai dashi da mahaifiyarsa halinsu kusan ɗaya ne, kaifi ɗaya ne wasu irin bauɗaɗɗun mutanene, koda yake in mukayi la’akayi da cewa mahaifiyarsa baturiya ce, sannan kuma ba musulma ba, yanayin rayuwarmu da tasu ba ɗaya bace, amma gasky munsha Wahalar fatima fiye da tunanin mai tunani, ta azabtar damu saboda muna kwakwar ƴa’ƴanta, har yau fa ita bata yarda cewa Allah ɗaya bane, taƙi karbar musulunci, kuma bata yarda cewa ƴa’ƴanta sun musulunta ba, in har zasu taka suje wurinta to fa basu ba yin sallah ko karatun qur’ani sai dai in ba dasaninta ba, dakyar fa aka samu rafayet ya musulunta har yakai shekara 20 aduniya ba shi ba musulmi bane,

 

ta tsagaita da maganar tana sauke ajiyar zuciya, gaba ɗaya sauraronta sukeyi, musamman Aunty babba da Amani su da basu son komai ba game da su rafayrt ba,

 

Su twins kuwa da fawan jikinsu yayi sanyi domin ana magana ne akan mahaifiyarsu,

 

Aunty babba tace “nikam inaso nason wacece fatiman nan, ya akai abba ya aure ta ba tare data karbi addinin musulunci ba, Kuma har akayi gangancin barin ya’yanta suyi koyi da addininta ina nufin rafayet da ki kace yakai 20 yrs batare da yakarbi addinin musulunci ba, sannan ina fatiman take a yanzu, don ni ban ta6a ganin ta ba,’

 

Asalin family ɗinmu Hausa fulani ne, mahaifin.mu bahaushe ne haifaffen garin zariya, mahaifiyarmu kuwa bafullata ce yar jihar damaturu, Haɗuwarsu tafarko a barikin sojoji na kaduna state Allah ya haɗa jininsu har takai su gayin aure ❤

 

Mu uku ne a wurin iyayenmu banban cikinmu Shine hussain wato (Abban sojoji) tagwaye ne su Allah yayiwa hassan ɗin rasuwa tun kafin su mallaki hankalinsu, Akwai tazarar shekaru a tsakanin mu sosai dashi, shi ne nafarko sai kuma ni azeema daga ni kuma sai ƙanin mu gaba ɗaya, wanda shine autanmu mun girme shi sosai, wato ABUSUFYAN wanda ynx yake zaune a Ƙasar turkey,’

tun yana 20years a duniya, wan mahaifiyarmu ya bashi auren ƴarsa maryam, yarinyace mai ilmin addini sosai ga hankali da natsuwa, maca ce mai saukin kai, bata ɗauki duniya da zafi ba,

 

Itace matarsa ta farko, sun sha sosai kamar laila da majnun, domin mu kanmu shaida ne akan hakan, duk in yana gari tashiga tarairayarsa kenan, idan aka turasa aiki kuwa nesa ba ƙaramain shiga damuwa take yi ba, duk tabi ta susu ce,

 

Abban mutunne mai son ƴa’ƴa koda yake bashi kaɗai ba, mu dukkan mu haka muke da son ƴa’ƴa zumuncin family ɗinmu yana da ƙarfi sosai, bama wasa da sada zumunci,

Cikin ikon Allah maryam ta samu ciki, kowa ya hau murna musamman ammin mu grandma ɗinmu, dayake maryam mutuniyarta ce tana sonta sosai kasancewarta yar yayanta modibbo,

 

Haihuwa tafarko maryam ta haifo kyakkyawan ɗanta, santalelen yaro yaci sunansa Ishaq (wato general ishaq) daga shi kuma sai Abbas wanda ynx yake rike da mukamin colonel general, daga Abbas sai brigadier general Abuhaisam gashi nan zaune kuna ganinsa, daga shi kuma sai major genaral Osman dukansu tazarar 2 years ne a tsakaninsu su duka, daga shine maryam ta ɗan huta,

 

Bayan nan ne tafiya ta kama su Abba izuwa ƙasar america, an tura su zuwa halartar wani special training na sojoji da za’a gudanar, da courses na dabarun aiki,

 

Hankalin maryam ba ƙaramin tashi yayi ba, jin za’a tura mijinta ƙasar turai, tsoranta kada wata tagansa ta liƙe masa Acan, saboda yana da farin jini sosai, 😇

 

Aiko hakance ta faru domin kuwa da zuwan su Abba u.s wata zankaɗeɗiyar budurwa kyakkyawar gaske ta ƙella ido tagansa taji cewa duk duniya bawan da take so sai shi,

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button