Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 7

Sponsored links

“Good, inaso ki manta da duk wani kunci da kika shiga na rayuwa, study and make your daddy proud okay?”……

Gyada kai tayi tana murmushin daya kasa barin fuskarta, ta dade bataga mutum me kirkin daddy ba a rayuwarta….

Shigowar momma ne ya katse conversation dinsu, sakon ta mika masa yace ta zauna….

“Gobe zamuje dake muyi enrolling dinta a school da islamiyya, inaso mu tsaya akan al’amarinta kamar iyayen da suka haifeta zasuyi”…..

“Insha Allah alhaji, yanda kace haka zaayi”…

Momma ta fada tanaji kamar zuciyarta zata fado wai su tsaya mata kamar iyayenta, ko ya’yansa na cikinsa be musu haka ba, saidai taga kamar hakan ze kara mata kusanci dashi, saboda haka zatayi using advantage din wajan cusawa mama bakinciki……

“Ya kamata muje ayi mata shopping ma naga batazo da kaya”..,,,

“Yauwa kin kawo shawara me kyau, shiyasa nake sonki wallahi, Allah ya miki albarka”…..

 

“Ameen mijina!”…..

 

“Ki mayar da ita ta samu ta kintsa, in kin gama saiki dawo ko?”….

 

Ya fada yana kashe mata ido daya kasancewar itake dashi a ranar…..

 

Kashemasa ido itama tayi ta rike hannunta suka fita daga part din…..

 

Bata nuna mata komai ba tasata tayi wanka tayi sallah, ta kuma bata abinci sannan ta kaita wani spare room tace ta kwanta, part din Alhaji ta koma suka raya daren cikin aminci, alhaji sai nan nan yake da ita……..

Tinda momma ta tafi ta barta ta kasa bacci, babu abinda takeso illa taga tasha kwalbar codeine dan shi kadai ne ze iya sata bacci a halin da take, da abin duniya ya isheta sai ta tashi da niyar fita ko Allah zesa ta samu me bata codeine kamar yanda wanchan ya bata sigari dazu, saidai kash tana zuwa taga kofar parlourn a garkame, ashe momma ta kulleta ta waje kamar tasan zata fita……

Komawa dakin tayi tanajin yanayinta na dan chanjawa, chan kuma saita fara birkicewa saboda tanaso tayi baccin amma ta kasa, kuka ta hauyi me karfi amma ba wanda ya jiyota ballatana akawo mata dauki, haka ta cigaba da kukanta har akayi kiran sallar asuba lokacin idonta yayi ja kamar gaurashi, tayi kukan tayi kukan harta gaji, da kyar ta daure tayi sallar asuba dan lokacin zazzabi harya fara kamata……

Karfe bakwai momma tashigo part din, sosai hankalinta ya tashi a halin data ganta dan alhaji yace da wuri zasu fita, idan yaga yarinyar a haka ai sai ya dauka wani abun aka mata bayan jiya har kyauta ya mata……

Tambayarta ta hauyi meya sameta saidai kememe taki cewa komai har ran momma ya fara baci, daurewa tayi ta sata tayi wanka ta gyara mata fuska dukdan kar daddy ya gane komai sannan ta mata breakfast ta bata taci tanata lallabata, a haka alhaji yazo ya samesu ya kuma ji dadin yanda momma keta nan nan da ita, sai hankalinsa ya kwanta ya bawa momma yarda dari bisa dari……

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button