Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 6

Sponsored links

Haka mama ta cigaba da zaginta ta inda take shiga batanan take fita ba, itako batasan ma anayi ba dan tariga tayi nisa batajin kira………

“Ashe baku da kirki baku da mutunci! Ince a kula da yarinya kafin in dawo sai kuka mayar dani kamar shashasha kuka banzatar da maganata, kunsanni sarai bana tolerating nonsense toh duk zanyi maganinku wallahi!…..

Alhaji Ibrahim da shigowarsa kenan ya ganta a inda ya barta ba wani alamar chanji ya fada rai a bace…….

Da sauri momma ta tashi ta kamo hannunta tana fadin;

“Allah ya wuci zuciyarka Alhaji, tuba muke”…..

Sannan tayi part dinta da ita……..

Bece komai ba mama tazo itama zata bada nata hakurin ya daga mata hannu yana nunamata hanyar kofa…….

Abincin momma ta bata dukda batayi niya ba saidan gudin abinda zeje ya dawo dan tasan hankalin alhaji na kan yarinyar yau, koda ta bata abincin bata taba ba ta shiga bacci a gurin, tabe baki momma tayi ta cigaba da sabgoginta……

Bayan sallar isha ya sake tarasu a part dinsa, kashedi da jan kunne ya musu akan kula da yarinyar sannan ya dankata amana gurin momma dan yafi yarda da ita gashi ita ta fara daukan yarinyar dazu….

“Alhaji duk munji sharudanka kuma Insha Allahu zamu kiyaye, saidai baka fadamana wacece ita ba?”….

Bayan sallar isha ya sake tarasu a part dinsa, kashedi da jan kunne ya musu akan kula da yarinyar sannan ya dankata amana gurin momma dan yafi yarda da ita gashi ita ta fara daukan yarinyar dazu….

“Alhaji duk munji sharudanka kuma Insha Allahu zamu kiyaye, saidai baka fadamana wacece ita ba?”….

Momma ta tambaya…..

“Wannan ba hurumunku bane, kawai kuyi abinda na saku, zaku iya tafiya, yauwa ki turomin yarinyar yanzu!”……

“Amma alhaji me zatazo tayi yanzu yarinyar daba muharramarka bace!”…..

“Bakida hankali ne?, ni kike gayawa me zanyi da ita, toh inyi me da yarinya karama kamar wannan, fita ki bani guri hafsah, fita nace!!”…….

Alhaji ya fada cikin tsananin bacin rai, ya rasa meyasa kishi kesa wasu su rasa lissafinsu kamar dai hafsah…..

Kamar yanda ya umarta haka momma ta kawota part dinsa bayan ta samu ta tashi da kyar daga baccin datake tin dazu…..

“Wai harta kwanta? Naga kamar daga bacci kika tasota ko?”……

“Eh wallahi, amma tindazu take baccin, naga kamar a gajiye take shiyasa na kyaleta”…..

Momma ta fada kamar gaske….

“Kwarai a gajiye take, kin kyauta da kika barta tayi baccin, nagode sosai uwargida sarauniyar gida”….

Murmushin yake tayi kamar taji dadin abinda yace nan ko ita kadai tasan abinda takeji a zuciyarta…..

“Keda kike san ya’ya mata gashi Allah ya baki, sai ki riketa amana kamar yarki, sai kiga Allah ya baki lada”…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button