Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 46

Sponsored links

Tracker dinshi ya fito dashi ya gwada tracking wayar offline saidai kash an kashe abinda ze bawa tracker din access to wayar, abinda kuma be sani ba shine Umm ce ta kashe ko kuma ita fatima zainab dince?…

 

Inko fatima zainab ce lallai she’s too smart, sai kawai ya yanke shawarar nemansu da kansa har ya gansu tinda an tabbatar masa suna dubai…..

 

Yaso ya bari zuwa gobe ya fita ya fara nemansu sai zuciyarsa ta kasa daurewa, haka ya fito a daren ya fara yawan nemansu, kamar zararre haka ya dinga zuwa layi layi, shago shago a kafa yana nemansu, babu lungu da sakon daya gani dabe shiga nemansu ba, yayi tafiya yafi na hour uku amma babu kome kama da su, haka ya daure ya cigaba da bawa zuciyarsa kwarin gwiwa akan lallai ze nemosu duk inda suke, yana tafe har aka kira sallar asuba, a Grand Bur Dubai Masjid daya kasance nearest mosque a lokacin ya shiga yayi sallah, haka ya zauna yayita kwararo addu’a Allah yasa ya gansu yaci ubansu, kamar zararre haka ya dora daga inda ya tsaya bayan ya fito daga masallacin, ya shiga abun hawa kuma yaki dan gani yake sai yafi ganinsu a kafa, haka yayita shawagi a garin dubai yana nemansu, kawai sai tsintar kansa yayi a ‘Opera Gallery Dubai’, zaro ido yayi yana mamakin yaushe ya kai nan, gurinda sai kayi tafiyar 400km daga gidansa sai gashi yayi wannan uban tafiya be sani ba……

Wata kyakkyawar shawara zuciyarsa ta yanke masa, ba bata lokaci ya shiga cikin opera gallery, guri ne me dauke da zane kala kala na gani na fada da akeji dashi a kasar dubai, drawing session ya shiga yace a bashi materials, sunata mamaki me zeyi dashi, haka aka kawo masa duk wani necessary abu na standard drawing, ba bata lokaci ya nitsu ya shiga zana duk wani features na fuskarta kamar yanda yake haddace akansa koda yaushe….. Ya kai one hour yana zanen kafin ya gama amma it was so perfect kamar ba artificial ba, kallon zanen ya shigayi with so much adoration kamar ita yake gani a zahiri, murmushi ne ya subuce masa kamar tana wajan yace;

“Ashe haka kike da kyau? Can I say you’re the most beautiful girl I’ve ever seen? Naaah don’t feel yourself bana kallon mata bare in sani”……..

“Where are you? Meyasa zakibi namiji ku gudu? Why? Why baby girl!! Allah idan an daura aurennan saina kashe shi, I don’t mind you being karamar bazawara! Barema I have a strong feeling that baa daura ba!!”…..

Ya sake fada yana jin yanda ransa ke baci, daga drawing din yayi ya cigaba da kallo yanata masifa kamar da ita yake……

Tafi yaji anayi daga gefensa ya dakatar da masifar da yake ya dago yaga su waye, ganinsu yayi a tsaye sai kallon drawing din da yayi suke kamar su kwace daga hannunsa, tafi suka sakeyi cikin turanci wani ya mika hannu ze karbi zanen yana fadin;

“This is so perfect habeebee! Like beyond perfect! Can we pls have a copy of this?”…

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button