Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 29

Sponsored links

“Au yanzu kuma tayi yarinya ta fara soyayya? Ina cewa kayi zaka mata aure dama? Tinda ga wanda takeso sai ka aura matashi”….

“Wallahi bazata aureshi ba Umm, yes she’s too young for love kamata yayi ta maida hankalinta kan karatunta! Ko auren zan mata bazan aura mata shashasha irinta ba bare na fasa mata auren, karatu nakeso tayi”…….

Yana fadin haka ya fice daga parlourn….

“Wai meke damun brain din yaronnan ne Umm?”……

“Hmmm mu tayashi da addu’a kawai, I’m speechless”…..

Lallashin fatima zainab data fara kuka bayan fitarsa suka hau yi, birkice musu tayi ita saita bar gidan bazata zauna da wannan mugun a gida daya ba dan dagaske fushinsa ya tsoratata, hakurin duniya sun bata taki hakura sai kuka take musu ita bazata zauna ba, Umm ce ta kalli mami tace;

“Innalillahi yanzu ya zamuyi? Kinga abinda ya janyo ko”…..

“Huh meye abunyi banda mukirasa yazo ya san nayi tinda shi ya jawo komai!”……

“Bari in kirasa”…..

Fita Umm tayi ta tafi part dinsa da beda wani tazara dana mami, samunshi tayi yanata safa da marwa kamar wanda aka yiwa wahayin masifa, harararshi tayi tace;

“Tace bazata zauna a gidannan ba, sai kazo kasan yanda zakayi da ita!”…..

Ta fada tana ficewa daga parlourn……

Da sauri yabi bayanta dukda har lokacin be wuce ba, so yayi yaki zuwa ya nuna musu yayi zuciya da ita taje duk inda taga damar zuwa sai zuciyarsa taki bada hadin kai kawai yabi bayan Umm……

Kukanta ne ya fara masa iso tin kafin ya karasa parlourn, sosai yaji zuciyarsa ta karaya akan yanda yaga tana kuka, shida ko wani ne yasata kuka sai inda karfinsa ya kare sai gashi shine ya sata kuka da kansa? A kuma lokacin ya fara nadamar yunkurin dukanta dayayi har yakai ga zuba mata belt sau daya, meya aikeshi meya kaishi? Yanzu da badan an kwace belt dinba me zai faru?…. Girgiza kai yayi ya tsuguna daidai inda take, su mami na ganin haka suka haura sama suka barsu su karata……

Hannunsa yasa ya goge mata hawayenta sannan cikin kwantar da murya kamar bashi ya gama masifa dazu ba yace;

“Stop crying baby girl! Banaso kan ki yayi ciwo”…..

Bige hannunsa tayi tace;

“Bazan dena kukan ba kuma bazan zauna a gidannan ba!”…..

Pecking hannunta yayi ya dauko belt din yasa matashi a hannu yace;

“I know I did you wrong, gashi ki rama ko guda nawa kikeso, amma dan Allah karki kara cewa bazaki zauna a gidannan ba”…..

“Wallahi bazan zaunaba, kai mugune”…

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button