Hausa Novels and Stories

Matar Damisa Book 1 Chapter 2

Sponsored links

Bayan na sanar masa bai nuna mun 6acin ransa ba amma sai dai yaki amincewa da Aurena,

Kinsan mai ya cemun??

Ta karasa maganar tareda tambayar Ayush.

Girgiza Kai Ayush tayi tareda ‘kura Mata ido cikeda mamaki take kallon mahaifiyar tatan,

Ta cigaba da cewa “naji takaicin maganar daya gaya mun”

Hmmmm! Taja ajiyar zuciya sannan tace “cewa yayi yabar Matarsa a Nigeria tare da ‘Dansa, baya bukatar ‘Kara Aure saboda gudun matsala!

Sannan yace “zai tafi Dani gidansa a matsayin er Aikin matarsa,

Ayush zaro Manya-manyan idanuwanta tayi waje tana kallon mahaifiyar ta, ta rasa abun cewa

Sai ji tayi Umma tace “a lokacin na kudurta a raina cewa saina rabashi da matarsa, saboda Ina matukar kishinsa, kuma sai nabi ta hanyar dazan bi na Aure shi,

Na bishi a hakan har muka komo Nigeria, ya gabatar dani a wajen matarsa Doctor Fateemah mutumiyar kirki, batada tashin hankali, sai ‘Dansa mai suna Junaid karamin yaro ne lokacin baifi 10yrs ba,

Alhajin bai 6oyewa matarsa komai ba ta yanda muka hadu, sai dai bai sanar mata da cewa ina sonsa ba,

Na fara gabatar da Aikin gidan a matsayin er Aiki suna biyana salary duk wata”

Umma ta dakatar da labarin tayi shuru kamar mai tunanin wani abu sannan tasau murmushin takaici

Ta cigaba da cewa “a lokacin na nemi wani hatsabibin boka babban matsafin duniya, ta hanya wata shu’umar mata wacce muka hada kawance da ita,

Tafiya mai nisa mukayi domin zuwa gurin bokan ni da kawata,

Kuma mun sameshi amma guri ne mai hatsarin gaske ba kowa ne yake zuwa dajin ba sai mai karfin ikoh,

Na sameshi da maganar Alhajin nan, Bokan yayi wani irin matsanancin Dariya mai rikitarwa sannan ya sanar mun cewa

Zan mallaka masa Abu uku ne kafin ya biya mun bukatata,Na farko zan bashi kudi 100Bs,

Na biyu zan mallaka masa jinin yaro namiji domin biyan bukatarsa na daban ,

Na uku zan bashi kaina, ma’ana yayi lalata Dani,

Duk na amince masa saboda nima inason bukatata ta biya,

Sai dai Abu na farkon daya fad’a shine zai ban wahalar samu wato 100Bs,

Bayan mun bar dajin hotel muka Kama saboda garin yayi nisa sosai,

Anan ne nayi shawara da kawartawan akan batun kudin

Ta sanar mun cewa wannan bazaiyi wahalar samu ba, nayi mamakin jin hakan saboda kudi ne mai yawan gaske,

Daga baya tace mun zata iya bani duk kudin kyauta amma saina bata Abu daya,

Na nuna Mata cewa komai ma zan iya bata indai zan samu kudin,

Ashe cikakkiyar er lesbian ce (madigo)

Ban nuna Mata komai ba sai cewa nayi na Amince “na mallakawa ‘katon boka mah balle ke kawata”

Taji dadin wannan furucin nawa

Haka muka aikata madigo cikin jin dadin juna ba tareda fargaban komai ba, ta mallaka mun kudaden nan nakaiwa boka, shima na bashi abunda yake bukata ajikina sannan na bashi yaron Alhaji wato Junaid,

Sai dai kash abun bakin ciki anan shine Bokon nan yana son haihuwa amma manyan Aljanunsa sun hanashi har saiya mallaka musu jinin yaro namiji kafin su bashi haihuwar,

Ya nemi Mata da yawa amma ba haihuwar, yaran da suke kawo masa jininsu baiyi dai dai da kalar jinin da suke nema ba shiyasa ya hakura da neman matan,

Sai akaina kuma jinin Junaid yazo dai dai da jinin da suke bukata,

Boka yayi matukar farin ciki sosai, ya kamu da sona hakan yasa ya ruguje duk wani tsafin da yayi don na mallaki alhaji, yace “bazan Auri kowa ba, kuma bazai Aureni ba saboda su basa Aure,

Bansan hakan ba sai da ciki ya fara 6illowa daga tumbina, na tsorita sosai,

Har cikin ya girma! shi kuma bokan ya haskaka madubinsa gareni duk wani motsina yana gani ta madubi, kuma duk abunda nakeso zai bani saboda cikin dake jikina,

Har Allah yasa na haihu jaririyar mace ba kowa bace face ke *AYUSHMAT*

Ayush suman zaune tayi jin mahaifiyarta ta ambaci ita diyar boka ce

Innalillahi wa inna’ilaihi raju’un,

Abunda Ayush taketa furtawa kenam,

“Umma kin cuceni, kin ‘kazantar mun da rayuwata, na shiga uku nah, wayyo Allah nah, Umma laifinki babba ne, kin gama da rayuwata, bayan ni er cikin shege ce hakan mah diyar babban boka iblis”

Cikin takaici ta zubawa mahaifiyarta ido, idanunta duk sunyi jaa tsabar zubar hawaye, ta lankwasa wuya ta zamo kalar tausayi, murya a sanyaye take fad’in “Umma ya rayuwarki a haka? Meyasa kika za6arwa kanki kalar ‘kazamar rayuwar nan , Gashi nima ya shafeni, Allah sarki Junaid yaro bai san komai ba gashi an jefa rayuwarsa cikin hatsari”

Umma Bara’atu gaba daya ta susuce, ta fita hayyacin ta, idanuwanta duk sun ‘kan’kance tsabar kuka, bakinta na rawa tace “Ayush kiyi hakuri, nasan na cutar da rayuwarki, naso ace kema kin zamo d’iya mai enci” kuka ne yazo mata mai cin rai.

 

 

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button