Hausa Novels and Stories

Idon Naira 5

Sponsored links

A hankali Zainab tafara girma tare da samun kulawa daga wajen Abbansu Malam Adamu wanda duk wata hidimi na Zainab shi ke yi tun dawowarta gidan Dan Zamanta a hannun Umma Hadeeza ya zama sunane kawai sbd bata san duk wata wahalar kulawa da ita ba sai idan Malam ɗin ya fita kasuwa ne kaɗai ta ke yi mata abinda ta ga za ta iya, amma daga wankan safe zuwa shiryata da bata abinci da duk wata hidimarta Malam ɗin ke yi da safe kafin ya fita sauran Kuma zatayi abinda taji zata iya Wanda bazata iyaba Maryamah tayi iya Wanda taji zata iya itama,

Idan ya dawo zai tadda tana buƙatar wani sabon gyaran haka zai zage ya sake mata wanka ya sauya mata shiga sannan su haɗu aci abinci yana bata abaki sbd bazata iya ci da kantaba.

Maryamah bata taɓa janyota a jikinta ko sau ɗaya ba bare ta hidimta mata,bata taɓa nuna so ko qi akan Zainab dinba yanda ta yi treating mahaifiyar Zainab lokacin tana raye haka take treating Zainab ɗin

 Hasalima ko sakin fuska daga gareta Zainab bata gani sai ya kasance ma tsoron Maryamah ya shigi Zainab ɗin ta yadda ko kusa da Maryamah bata son zuwa Dan gwara mahaifiyar Zainab din da batada irin kamewar fuskar Maryamah sosai.

Ummar ma sam bata janyota a jikiba saidaj Bata kame mata fuskarta sbd ganin bazatama iya wahalarda kanta da daure dauren fuska da damuwaba akan jinjirar yarinya hakama ba wani boyo ta fifita soyayyar ƴarta akan Zainab sosai da sosai Shiyasa Zainab din tun shekarun nata Basu wani tasaba gane batada uwa kuma ta taso da tsoransu da rashin sakin jiki da su har tayi girman fara zuwa makaranta saidai Abbansu na dawowa tana walwalarta da farin cikinta sosai kaman kowanne yaro.

Rashin kulawar umman Maryamah akan Zainab baya damun Malam kaman rashin kulawar Maryamah akanta da rashin shaquwa ko kaunar junansu..

Abin Yana tsananin damunsa da basa tsoro sbd Maryamah ita kadaice Yar uwarta dasuke jini daya yake Kuma fatar ta zamewa Zainab din gata idan sun hade kansu a gaba har zuriarsu,

Fatansa burinsa su zama tsintsiya madaurinsu daya har tsufa da zuriarsu,

shiyasa yake jin damuwa akan halin ko inkula da rashin kulawar Maryamah din akan Zainab.

yayi faɗa yayi nasiha har ya gaji ba wani sauyin arziki ya hakura ya zuba musu ido tare da cigaba da inganta rayuwar tasu da adduar hadin kansu su dukan.

Karshe dai kasa hakuri yayi ya dauko tsarin zaunawa dasu biyun idan har Yana gida to Yana tareda Maryamah din da Zainab Yana fira dasu tareda jansu a jikinsa sosai ko hakan zaisa kauna da shaquwar dayake fata su shiga tsakaninsu.

Umma Kuma tana ganin Zainab tafara girman da zata iya wasu ayyukan saita raba musu aiki wanda kusan ayyukan Zainab din sunfi na Maryamah yawa a cewar Maryamah karatunta yafi wahala tunda har yamma take kaiwa ita Kuma Zainab yanxu nema take Shirin shiga secondary.

Kafin ta tafi makaranta da safe sai tayi aikin shara da wanke wanke kafin ta tafi hakama tana dawowa sallah da kawai takeyi saita Kuma shara da wanke wanke da wasu Yan ayyukan ta wanke uniform dinta kafin taci abinci ta wuce islamiyya.

Tana qara girma kuwa hatta wankin umman da Maryamah ce keyi ya dawo kanta

Tana qara girma kuwa hatta wankin umman da Maryamah ce keyi ya dawo kanta

 

Maryamah ma umman tayi tayi tabarwa Zainab wankinta taringa yi Amma tace Sam Bata buqata sbd ita irin mutanen ne da idan basa son abu ko kaunarsa to ko wahalardashi basa iyayi sbd kadama komai ya hadaka dasu shiyasa ko aikin wahala Bata damu data bawa Zainab din tai mata ba saida idan batanan umma tabawa Zainab wankinta Amma indai tana Nan Bata so itace takeyin abinta.

Rashin sabo da haniya da rashin abokin hira a gida da bata da shi sai ya kasance Zainab din ta taso a miskili batada surutu ko rawar Kai ko makamancin hakan shiyasa ko a makarantar boko da islamiyya batada qawa ko daya Kuma daidai gwargwado tanada qwaqwalwar daukar karatu hakan ya qarawa malam qarfin zuciya akanta da sake dauke ido akan rayuwar dasukeyiwa Zainab din tunda Basu cutatar da itaba Kuma Basu fito sun furta mata qiyayyaba Kuma lurada qaunarta dayake bayyanarwa da tausayinta shike sake neman dagula Yar qaramar zaman lafiyar da akeyi a tsakaninsu sai kawai yaringa binsu da adduar shiriya su dukan har umman

Kuma tunda dai Zainab din na fira dashi harda dariya sosai ba laifi hakan ma Allah ya shirya masa su gashi dama Sam umma Bata taba yimata horon yunwaba abinci ake Bata yanda ya isheta tunda ubanta ke kawowa.

Maryamah tagama karatunta tuni harta gama service dinta aiki takeson farawa Amma abban nasu yaqi amincewa sbd shekarunta sun qanqanta da fara wannan rayuwar Dan hakan yabawa manemin aurenta damar fitowa ayi aurensu saita fara aikin nata acan.

Barr Asadullah Muhammed Ismail shine Wanda yake neman maraymah din da aure tun Bata gama karatu ba,

Shima tuzuru ne sosai Dan ya jima Yana aiki batareda yayi aureba harya fita cikin layin samari,

 

 

 

 

 

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button