Hausa Novels and Stories

Abban Sojoji Chapter 9

Sponsored links

mamaki ya ke ganin taƙi ɗauke eyes ɗinta akansa, kuma bata da niyar daina kallonsa, hannunta har rawa yake yi wurin ajiye spoon ɗin da ta ɗauko,

Lumshe idanunsa yayi a hankali yana ƙare mata kallo acikin zuciyarsa yana cewa “Ya Allah ka mallakamin wannan baiwar ta ka,’

 

A yayin da sehrish ke cewa”

 

_tsarki ya tabbata ga ubangijin daya halicci wannan kyakkyawar surar Junaid duniya ne_💋

 

_shigowar azmee ne ya dawo dasu daga wannan tunanin na ƙurawa juna ido kowa ya waske_

 

cikin fara’a azmee tace” junaid me ka ke bukata ne na kawo maka? naga baka ci komai ba,

A cikin zuciyarsa yace”kallon ta danake koshi nake Aunty azmee”

 

A fili kuma yace” nima cornflakes ɗin zan sha, a haɗo mun da fresh fruits’

 

“Junaid ba ka son cin abinci ko? Kafi son ƴan lashe lashe kamar Tukur”?

 

Wani irin murmushi ya saki jin abunda azmee tace har time ɗin idonsa nakan sehrish wadda ta mayar da idonta kan cheese burger ɗin dake gabanta so take ta ɗauka taci amma zuwan junaid yasa duk ta dabarbarce sai ƴan kame-kame take

 

“Aunty azmee ae we are the same ni da shi,’

Azmee tace “gsky saina haɗa maka da farfesu mai zafi zaka ji daɗinsa,’

Junaid yace “its ok am waiting,

zuciyarta sai faman ɗar ɗar take yi mata, kamar mara gsky koda yake ba gaskiyar ae,

 

Shi kam ya zuba mata ido yana kallonta, yarinyar ta kwanta masa a heart ɗinsa, just he is affected 💘

 

Azmee ce ta ƙaraso hannunta ɗauke da plate wanda ta zuba masa farfesun ganda aciki, ajiye wa tayi a gabansa, sannan ta koma ta Kawo masa fresh fruits ɗin daya bukata acikin wani haɗaɗɗen round tray,

sannan ta koma ta kammala haɗa masa corn flakes ta kawo masa,

 

A hankali ya furta “shukran aunty azmee’

 

azmee ta juya ta fice tana ɗan murmushi bata ta6a sanin cewa junaid Romeo bane na gaske sai da ya gane cewa reeshi maca ce ba namiji ba, ❣️

 

Ƙamshin farfesun gaban junaid ne ke ta faman kai mata hari, ɗagowa tayi tana satar kallonsa,

 

A hankali yake sa hannu yana ɗaukar gandar ta dahu tayi tubus taji kayan haɗi na kamshi, irin wadda daga kasa a baki zata dagargaje😋

 

A hankali yake turawa abakinsa yana tauna, ganin bai kara ɗagowa ba yasa tayi saurin wawurar burger ɗin tana turawa a baki,

 

Muryarsa ce ta katse ta “Ki ci a hankali,” ya furta yana ɗan smiling ashe ya ɗago bata sani ba

 

kaɗan ta gutsara ta maida ta ta ajiye, hot dog ɗin ta dauka tana ci,

 

a yayin da shi kuma ya ɗauki spoon yana shan cornflakes ɗin da azmee ta kawo masa,

 

Wani tunani ne ya faɗo masa aransa a lokacin da yake kallon sehrish wadda take ta faman ƴan kame kame,

Bin ta da kallo yayi aransa yace ” Wani abu na ban mamaki nikam, ko ya aikai take matse boobs ɗinta, suyi flat tamkar babu, dama Allah yasa su 6ace muga yarda zata yi……..

 

Shi kansa baisan dariya ta kubuce masa ba, har ya fetsar da cornflakes ɗin dake bakinsa, zuba mishi ido sehrish tayi gaban ta na faɗuwa tsoranta kada ace wani abu junaid ya ganu wanda zaisa ya gane cewa ita maca ce,😳

 

Sai faman tiƙar dariya ya ke yi ba kakkautawa, sam ya gaza stopping kansa,

 

Tamkar tv haka ta ƙura wa junaid ido yana dariya, fararen hakoransa jere rass take kallo ga ƴar wushiryarsa siriri ya,

 

ganin ya kasa controlling kansa ya sa ya miƙe ya kama hanyar fita yana ci gaba da dariyar,

 

Abun ya bata mamaki, ganin ya tashi yana ta dariya gashi baici abun kirki ba, anya junaid yana da lafia kuwa? Ko dai yana da psycriatric disorder ne?

 

daga bisa ni ta ta6e bakinta alamar i dont care taci gaba da shan abunta,

 

Bedroom ɗin abbansu ya wuce directly, a hankali ya tura kopan ya shiga, samun shi yayi a tsakiyar gadon ya baje abunsa, ya warware,

Murmushi ya saki ganin abban nasa, har cikin ransa yaji daɗi ganinsa ya dawo cikin ƙoshin lafia,…

 

“Lallai abba abu yayi kyau, shine an dawo ko a neme ni, aiko yanzu baccin nan naka zai ƙare,’

 

Ja da baya yayi sannan ya watsa a guje ya faɗa saman gadon sai ajikin abban nasu a firgice cikin magagin bacci abban ya rinƙa faɗin “a miko bindiga 6aro ya shigo ‘

 

fashe wa da dariya junaid ya yi, yana kallon abban nasu wanda idonsa ke a rufe yana ta faman sambatu,’

 

tabbas yaji nauyin mutun akansa, amma sam ya gaza buɗe eyes ɗinsa sbd a gajiye ya ke,

 

Cikin rashin imani junaid yasa hannunsa yana gwale masa idanu, sunyi ɗan ja, biji-biji yake ganin junaid sai faman zabga murmushi yake

Cikin nishaɗi ya ce “Abba its me your heart beat, i came here to disturb u, 🤣

 

a hankali abban ya idasa buɗe idanunsa, a firgice ya yunkura ya janye junaid gefe ɗaya, ba ƙaramin tsorata yayi ba, saboda idonsa wani farin aljani nuna masa sai da ga baya gane cewa she junaid ne,

 

“Yanzu ka kyauta ? dama ina ji an hau saman jikina nasan cewa kaine, duk duniya babu maiyi mun haja sai kai,’

 

“Cikin shagwa6a junaid yace “ka dawo baka neme ni ba abba,’ ya ƙare maganar yana zumbura masa baki,

 

yatsina fuska abban yayi yana kallonsa aransa yana cewa ” ynx fa sai yace zaiyi mun kuka shi ala dole gabu auta, bari na jaraba shi nagani ya canza ko hanyarzu yana nan yadda na barsa,

 

ɗaure fuska yayi tare da nuna ma junaid hanyar fit yace “kai tashi ka fice mun bana son takura jarababbe,’

cikin yanayin mamaki junaid ya ce” abba Ni kake ce ma jarababbe? Kadawo baka neme ni ba kuma shine kake korata ?

 

Abba yace “ka ga tashi ga fice mun tunkan nawaje suji mu,’ ya faɗi yana kara tamke fuska,

 

.ganin cewa dagske abban nasu yake yasa ahi tashi jiki a sanyaye ya sauka daga saman bed ɗin ya isa bakin kopa, bai bude kofan ba tsayawa yayi yana jiran abban ya bashi hakuri,

 

ɗan juyawa yayi da kansa ya saci kallin abban nasu wanda ke zaune tsakiyar gadon, haɗa ido sukayi lokaci guda 👀

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button