Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 34

Sponsored links

“Wallahi nafi karfin inyi kishi dake,kuma aurenmu nida alhaji mutuka raba takalmin kaza,baki da labarin sai yanda nayi da alhaji yanzu”

Mama ta fada tana fuzgo maganar cikin tsoro da fargaba…..

Wata muguwar dariya fatima zainab tayi tace

“Au haryanzu baki dena biye biyen boka da malamai ba? Toh ki zuba ido ki gani,ba boka ba mallam amma wallahi sai dayan biyun abunda na fada ya faru,bazanyi kaffara ba kuma”…

Zaro ido mama tayi jin abinda tace,cikin kidimewa a ranta tace nashiga tara ba goma ba ya akayi yarinyarnan tasan ina biye biyen malamai?,mazewa tayi tace

 

“Nima ba boka ba mallam kuma duk abunda kika fada baze faru ba”….

 

Sake fashewa da dariya tayi tace

 

“Lallai wuyarki ta isa yanka,ke a ajiye batun alhaji ya sakeki ma,ki saurari kayan fadar kishiya nan da sati daya!”…….. Ta fada tana ficewa daga part din….

 

Ya dade be jisa a cikin tashin hankali irin wannan ba,sai ya rasa mezai dafah yaji dadi,gashi mutumin ya gudu kuma ya rasa ta ina yabi…. Tinanin kiran Deen ne ya shigo kansa,yayi maza yayi dialing number amma sai tayita ringing be dagaba,fita daga gidan yayi yana tinanin ina ze nufa yanzu,yasan kuma be isa yaje gidansu a yanzu ba,yanke shawarar komawa abuja yayi,ya tafi airport ya siya ticket fortunately ya samu jirgin daze tashi yanzu…..

 

Yana isowa abuja ya sake trying number Deen,Allah ya taimakesa ya dauka a lokacin….. A rikice yace

“I’m safe,stop calling me,I don’t want to implicate you”…. Yana fadin haka ya kashe wayar….

 

Sai a lokacin hankalin sameer ya dan kwanta,duk yanda akayi kenan Deen yasan da plan din tinda har bayaso yayi implicating dinshi,yasan kuma Deen ze dauki action akan abun as smart as he is……..

 

A nitse ya cigaba da fitowa daga airport din,kamar ance juyo ya hango khaleel rike da traveling bag alamun dai yanzu ya diro kasar… Wani farinciki ne ya kamasa ganin yanda Allah ya kawo masa khaleel cikin sauki,dama ze kirasa a waya,sai kuma gashi sun hadu face to face…….

 

Daga sama khaleel yaji anyi hugging dinsa,juyowa yayi da sauri yana tinanin waye haka,mamaki yayi ganin sameer,take ko ya hade rai……..

Wani huge smile sameer yayi yace

 

“Bro abun ya kai har haka?,kana ganina ka hade rai?”….

 

“Abun yafi haka ma” khaleel ya fada ba alamun wasa a fuskarsa…..

 

“Toh Allah ya huci zuciyarka,yanzu kai kana tinanin duk abinda na fada gaskiya ne? Haba dude yama zaayi inso yarinyar dana san kadade kanaso,kofa ganinta banyi ba ranar kawai nayi creating abubuwa dana fada ne dan in tsokaneka,sai kuma naga ka mayar dashi babba, abunda yasa na kara tunzuraka kenan amma wallahi har cikin raina wasa nake,trust me kaima kasan bazan iya maka wannan betrayal din ba,dama kuma zan kiraka in baka hakuri wallahi”…..

Sameer ya fada looking so remorseful…..

Numfasawa khaleel yayi,har cikin ransa ya yadda da abinda da sameer yace,dan dagaske beyi tinanin sameer ze iya haka ba,in wani ne yace mishi sameer zeyi masa haka baze yarda ba,kuma har a yau ya kasa believing sameer ze iya masa haka,sai kuma Allah yasa sameer yayi clearing komai,ya kuma tabbatar masa da wasa yakeyi,wani sanyi yaji a ransa kamar anyaye masa duk abinda ke damunsa….

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button