Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 65

Sponsored links

Wani irin sanyi da nitsuwa deen yaji yana saukar masa saboda yanda sautin muryarta me dadi ke karatu cikin kira’a me dadi cike da kwarewa, koda wasa be taba tinanin zata iya karatu haka ba, ya dade beji murya me karatu me dadi irin nata ba, amma be yadda ya sakankance ba dan yana kiyaye duk wani harafi da take fitarwa har ta fara karanta suratul baqarah cikin tattausar muryarta……

 

Sai da ta karanta izu biyu yaji muryarta ta farayin kasa kamar me jin bacci sannan ya dakatar da ita yana murmushi yace;

 

“Masha Allah mallama zahrah, anya bazan bude miki islamiyya ki fara karantarwa ba kuwa?”….

 

Dariya tayi tana rufe fuska….

 

“Honesty I’m really impressed baby girl! Allah yayi albarka, tashi kije ki kwanta”….

 

Ya fada yana kallonta lovingly, dagaske bata taba burgeshi ba irin ranar……

 

Mikewa tayi tayi masa sallama ta tafi, ita dakanta sai take jinta wani iri saboda yau ce rana ta farko da suka taba rabuwa lafiya ba fada ba tsawa ba komai, sai taji hakan ya mata dadi….

 

Da farinciki yan gidan suka tashi saboda sanarwan zuwan mutan maiduguri da su uncle A mutan Dubai….. Sosai gidan ya kachame da gyare gyare da girke girke kamar wani babban taro za’ayi, ita kanta baby tee farinciki take sosai kamar ta sansu……

 

Tinda safe suka fita da mami da umm lokacin saif yana bacci be sani ba, fashion house din mami suka fara zuwa mami tace baby tee ta zabi duk wani choice of kaya da takeso, kasa zaba tayi mami tace kawai ayi mata packaging duk wani sabon design din kaya da yake gurin including varieties of abaya, tafiya sukayi saboda kayan sunyi yawa gashi sai an rage mata wasu, wasu kuma sai an kara kawai mami tace a kawo gida later, daga nan mall din umm sukayi, nan ma shopping spree umm tace tayi ta zabi duk abinda takeso kana daga kan turaruruka, undies, chocolates da komai da komai…… Daga nan kuma suka wuce wani beauty parlor aka musu manicure da pedicure, gyaran kai da kiso, babu yanda umm batayi ba akan akayiwa baby tee kitso tace ita bataso a mata gyaran gashin kawai, karshe da taga umm ta takura tace ita jan lalle takeso, ai kuwa aka mata irin me yankan celotape me shegen kyau na hannu da kafa, ana gama lalle tace ita a cire tagaji, umm tace bata isa ba ai tinda tace tanaso sai yayi awa daya sannan za’a cire, tanaji tana gani sai gurin la’asar aka cire tukunna, ba karamin kyau lallen yayi akan farar fatarta ba, sai ya kara fito da kyan hannayenta da kafafunta, suda kansu masu lallen sai koda lallen sukeyi, su umm ma saida sukace masha Allah dan ba karya lalle yayi kyau….. Sallah sukayi sannan suka wuce gida……

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button