Hausa Novels and Stories

Gidan Uncle Page 7

Sponsored links

Kallonta Hajiya ta tsaya tanayi kallo irin na qurullah tana mamakin tsananin ramar da tayi sai wani haske da idanu zuru² kamo hanunta Hajiyan tayi cikin tsoro tace “ya subhanallahi Umaimatu meye ya lalataki haka kinga kuwa yadda kika rame Baby meye yake faruwa ne?” Ta tambaya tana shiga dakin tana qare masa kallo komai dake saman gadon anyi watsi dashi qasa ga bra dinta nan da Shortnicker dinsa a zube a qasan gadon.

A kunyace ta sunkuya ta debe kayan ta nufi bathroom domin tasa a worshing machine ta fito har yanzun kallonta Hajiya takeyi a mamakance dawowa tayi ta sunkuya kusa da qafar uwar tata kuma surukarta tace “sannu da zuwa Hajiya wlh banaji dadine shiyasa duk na rame amma yau da dan sauqi tunda na danci abinci” kwafa Hajiya tayi tace “ai nasan bakida lfy amma ba iyakar rashin lfyr ce ta kadar dake haka ba dole akwai wani abu dake cin zuciyarki Umaimah babu dole a zamanki da Hameed idan har kinsan yana cutar dake tun wuri kafin ya illataki a raba aurannan saboda kema rayuwarki tana da muhimmanci a gurinmu”

Kallon Hajiyan tayi a dan razane tace “raba aurenmu kuma Hajiya akan me?” ajiyar zuciya tayi ta kama hanunta ta miqar da ita suka fita parlourn suka zauna Hajiya tace “nasan waye Hameed Umaimah amma bansan lamarinsa ya gawurta haka ba sai ranar da Jameelah tazo gdannan ta fadamin abinda ya faru tsakaninku me yayi zafi haka Umaimah shi bashida hankali ne baya duba yarintarki da kuma rashin sabonki gsky akwai cutarwa cikin lamarinku Umaimah koni dana shafe shekara 37 a dakin miji bazan iya wannan wahalar da kikeyi ba saboda nasan qarshen abin cutarwa ne ga kuma qaramin ciki shi baya tunanin ya jangwaleshi yabi kwararo”

Sunkuyar da kanta tayi tana wasa da yatsunta zuciyarta na kaikawo wai a raba auranta da Uncle to kuma shikenan itama sai ace ita bazawara tab Allah ma ya kiyaye gara taci gaba da zama dashi a hakan koda zaike kwana yana cinyeta, ganin batada niyyar yin mgn ne yasa Hajiya cewa“bazanyi miki dole ba Umaimah duk da nima karambani da shisshigi nane yake sani tsoma baki a tsakanin ki da mijinki tunda kin nuna min yafini matsayi a gurinki” share hawaye tayi ta kwantar da kanta a kafadar Hajiya daidai lkcn ya shigo gdan tsayawa yayi turus ganin Hajiya a gdan ya fara yan soshe² kunya yace

“Yanzu daga gdan nake Hajiya bakinan Aunty Jameelah ma batanan maigadi yake fadamin ta tafi jiya ko sallama babu” idonta ta mayar kan Umaimah tace “Eh fah tace bata qara zuwa gdanka ai jiya mijinta yazo sunka tahi” baiyi mgn ba ya shige dakinsa ya dauko system dinsa ya fito ya sake ficewa har yakai jikin motar sa ya juyo ya kira Umaimah ta miqe a kasalance ta fita inda yake ya ruqo hanunta yace “na roqeki da Allah ki riqe mana sirrin mu na fahimci Hajiya batason zamana dake idan kikaba da qofa zata rabamu Umaimah plz”

 

Yana fadin haka ya juya ya qarasa gurin motarsa ya bude yayi mata murmushi tare da kissing hannunsa ya watso mata dole yanda yayi din saida ya sanyata dariya ta juya ta shiga parlourn tana dariya, sakin baki Hajiya tayi tana kallon ikon Allah zama tayi kusa da Hajiyan ta zauna tace “Hajiya tuwon alkama nakeso miyan kubewa don Allah kiyimin Uncle zaizo ya karbar min” itadai Hajiya bakinta ya mutu sai binta kawai da takeyi da ido a ranta ta raya gara ma ta sawa kanta salama ta fita harkarsu kafin taji kunya miqewa tayi ta dauko wata roba da wani dakakken yajin daddawa ta bata tace “ga wannan yajin daddawa ne Daddynku yazo dashi daga Maiduguri sai ki dage wajan kula da kanki auran harijin namiji babu sauqi balle ke da kike da quruciya zakiji a jikinki kafin ki saba”

Itadai Umaimah kunya bata barta tayi mgn ba ta sake fito da wani magani ta bata tace “wannan hadin mune na shuwa yawwa ki rinqa yawan yin lemon apple yana qarawa mace ni’ima da dandano sosai zan sa Data nayi miki bayanin yanda zaki kula da kanki amma Ina qara fada miki akwai aiki a gabanki” gdy tayi mata ta rakata har gurin motarta ta shiga taja sukayi sallama tana daga mata hannu, saida taga ta qule sannan ta koma ta kwanta a saman kujera tanajin wani tausayin kanta da Uncle dinta yana bijiro mata shafa cikinta tayi tayi murmushi tanajin qaunar abinda ke cikinta a ranta tananan kwance har la’asar tayi sallah ta shiga kitchen ta girka masa abu me sauqi tayi wankanta tayi kwalliyarta cikin wani yeard me sauqin nauyi dinkin riga da siket tayi kyau sosai ta shiga dakinta dabai samu arzikin gyara ba ta gyara ta kunna turaren wuta ta fito parlourn daidai lkcn daya shigo parlourn shima tsayawa yayi yana kallonta murmushi a fili yace.

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button