Hausa Novels and Stories

Abban Sojoji Chapter 7

Sponsored links

Jiki na rawa ta ƙarasa gabanta cike da tsoro tace” husanna ina waya ?

 

Shiru tayi tana mazurai, hannu jahad tasa ta shaƙo wuyan rigar dake jikinta cikin matsanancin tashin hankali ta sake cewa “tell me where did you kept it ?

 

muryar na rawa husanna tace” wani kyankyaso ne ya hau mun saman kaine shineee…sai wayr ta faɗa cikin….’

 

“Cikin Uban me !? jahad ta tambaya cikin daka mata tsawa,

 

duk tabi ta gama firgita tata cikin takura tace “cikin ramin”

Aikuwa rai a tsananin bace jahad ta shiga kai mata bugu ta ko’ina, nan suka shiga dambe, faɗa ya katse me a tsakaninsu kai kace basu son junansu,

 

A ƙarshe jahad tasake ta cikin tsananin ƙunar rai tace”shikenan kinyi farin ciki ko? kada kiyi tunanin ina bakin ciki ne don kin jefa waya, ina bakin ciki ne saboda kinyi mana babbar asara, taimakon da zamu samu na kuɗi a siya miki magani mun rasa, sannan ƴar uwarmu ma mun rasa ta ! saboda daga ni har ke ba wanda ya riƙe numbar da take kira, sannan ita inta kira zata ji waya a kashe kinga shikenan tamu ta ƙare…..’

 

Zuƙunnawa tayi tare da fashe wa da matsanancin kuka, itama husannar koma tayi ta tsaya jikin bango tana shesshekar kuka jin jahad tace sun rasa ƴar uwarsu SEHRISH

A cikin wannan yanayin mara daɗi tsohuwa ta same su, shigowa tayi hannunta ɗauke da bakar leda wadda fura ce aciki ta samo musu don su sha tun safe rabonsu da abinci har izuwa yanzu da ake ta faman kiran sallar isha’e

 

hankali a tashe ta ƙarasa inda jahad take tana faɗin”lafiya meya faru ƴa’ƴan ne me kke wa kuka? Nasan yunwa ce ku kwantar da hankalinku gashi nan na samo mana ƴar fura musha,’

 

Jin wannan maganartata yasa jahad ƙara sautin kukan nata, tana kuka tana magana “ba wannan zararriyar bace nasamu sehrish tace mu tura mata acct number, nashiga gidan makwabtan mu wurin mamee nace taban nata acct number ɗin, sai da na anso ina shigo wa nasamu husanna wai ta jefa wayar cikin masai,”

 

Jin wannan maganar yasa tsohuwa sakin ledar furar dake hannunta, tashiga tafa hannu tana faɗin “Innalallahi wa’inna ilaihirraji’un shikenan ae kun gama dani shekara 10 kenan wayarnan da ita nake lallabawa ashe kune ajalinta, kun kyauta,’

 

tana faɗin hakanan ta shige cikin ƙuƙuƙun ɗakin nata ta rufo kopa, tunda suka ga hakan yatabbatar masu da cewa ran tsohuwa ya bace, saboda bata taba yi musu haka ba,

Gashi ɗaki ɗayane a gidan ɗayan ɗakin ya rushe sakamakon ruwan sama da akayi,

 

ga wani irin sanyi a wajen nan da nan jikin husanna ya soma kakarwa, hankali a tashe jahad ta tashi daga zukunnawar da tayi ta tunkare ta,

 

“zo muje mu lallashe ta tabuɗe mana ɗakin mu kwanta waje sanyi,”

 

Haka suka je bakin kopan ɗakin sukai ta kwankwasa wa amma tsohuwa tayi shiru babu alamar zata buɗe,

 

A ƙarshe sai dai suka rungume junansu suka ƙanƙame juna saboda sanyin dake akwai, wannan abun ya tuna musu da wani lokaci daya shuɗe a rayuwarsu mara daɗin ji 😭

 

Rashin gata baiyi ba a duniya

Rashin kwanciyar hankali yasa ko kwakkwaran bacci bata samu ba a daren jiya, tunaninta meyasa samu wayar tsohuwa ba’a samu tayi tarying amma swich off, hakan na matuƙar tayar mata da hankali tsoronta kar ace wani abu ya same su su duka,

 

Jiki a sanyaye ta kammala shiryawa ta wuce kitchen wurin azmi,

 

“Good morning aunty azmi”

 

ta faɗa tana kallonta, azmi dake faman gyare gyare a kitchen ɗin tace “morning baturiya hope u slept well”

 

yar dariya sehrish tayi ta shiga daga ciki tana faɗin “dame zamu fara ne?

dafe ƙirji sehrish tayi kamar wadda taji mugun abu tace”suwa!”?

 

dariya axmi tayi ganin yadda ta ɗan raxana,

 

“suna da yawa wasu yau zasu zo wasu sai gobe, daga ciki akwai chief of army staff wato Abban su junaid wanda zai dawo daga ƙasar chaina, amma shi gobe ne zai zo yau dai wasu daga cikin manyan ƴa’ƴansa dake other states ɗin zasu zo domin tarbarsa,

 

Da buɗan bakin sehrish sai cewa tayi “Babban yaya fa shi bazai zo ba,”?

 

girgiza kai azmi tayi tace”oh shirt! ni wannan babban yayan da kike ta faman zumuɗin gani bansan dalili ba,’

 

“Aunty azmi it’s just a question ba wani abu ba, naji kince manyan ƴa’ƴansa shiyasa na tambaya,’ ta ƙara maganar tana wasa da yatsun hannunta,

 

Kafin azmi tace wani abu junaid ya shigo da sallama, nan fa sehrish ta hau satar kallonsa yayi fes abunsa yayi dressing cikin suit black colour

dafe ƙirji sehrish tayi kamar wadda taji mugun abu tace”suwa!”?

dariya axmi tayi ganin yadda ta ɗan raxana,

“suna da yawa wasu yau zasu zo wasu sai gobe, daga ciki akwai chief of army staff wato Abban su junaid wanda zai dawo daga ƙasar chaina, amma shi gobe ne zai zo yau dai wasu daga cikin manyan ƴa’ƴansa dake other states ɗin zasu zo domin tarbarsa,

Da buɗan bakin sehrish sai cewa tayi “Babban yaya fa shi bazai zo ba,”?

girgiza kai azmi tayi tace”oh shirt! ni wannan babban yayan da kike ta faman zumuɗin gani bansan dalili ba,’

“Aunty azmi it’s just a question ba wani abu ba, naji kince manyan ƴa’ƴansa shiyasa na tambaya,’ ta ƙara maganar tana wasa da yatsun hannunta,

Kafin azmi tace wani abu junaid ya shigo da sallama, nan fa sehrish ta hau satar kallonsa yayi fes abunsa yayi dressing cikin suit black colour

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button