Hausa Novels and Stories

Zafin Kai 12

Sponsored links

Tsohon daya gama wanyewa dasu kullum shima a duk lokacinda ya bude bakinsa Benazir yakewa addua sbd itace mai fitowa ta basa,

Adduarsa kullum Allah yakaita matsayinda bata taba tinanin zuwaba tareda rayuwa mai Albarka da kwanciyar hankali tareda zuria dayyaba.

Exams dinsu aka fara dan haka hankalinsu ya rabu sbd kowa karatunsa yake kokarin maida hankali akai musamman Benazir sbd lectures da dama data ringa rasawa a lokutan sbd sumayyah da ciwon datayi bayan nan dan haka idan suka shigo makaranta sumayyah bata sake ganinta sbd Sosai karatunta ya samu ci baya shiyasa ta dage sosai kafin ta fadi Ababa ya kusa kashesu su dukan gwara a samu mai taimakawa wani acikinsu.

Sumayyah da kanta ya daure matiqa sbd exam din farko da suka fara babu abinda ta gane sunanta kawai ta rubuta sai questions din data maimaita masa a booklet bayan question daya babu abinda ta amsa said ta fito idanuwanta cike da hawayen tausayin kanta da yanda rayuwa zatai mata idan ta gama shekarun nan biyu duka a fail,

Wane mataki Ababa zai dauka akanta?

Siyar da ita zaiyi ga ‘yan qwaya da gaske ko me?

Inda suke zama ta nufa ta zauna ahankali tana sauke kanta qasa dukkanin jikinta na mutuwa hakama tsoron dake mamaye zuciyarta na qara bayyanuwa a kan fuskarta.

Haka ta jima a gurin tana saqa da warwara cikin damuwa har lokaci yayi suka sake shiga wata exam din nan ma kusan biredi ne ke dukan fanke bata tsinano abin arziki ba dan haka wannan karon tashin hankalinta da tsoronta qaruwa yayi sbd azabar datasha wancan karon data fadi exams din a hannun Ababa.

Tana fitowa kasa riqe zuciyarta tayi taje maboyarsu ta zauna hawaye na tsiyayo mata ta saka fuskarta tafin hannuwanta tana sakin kuka mara sauti gashi bazata iya fadawa Benazir ba ta sakata damuwa nata karatun ya fita kanta,

Bazata so hakan ba sbd ko yayane tanason Benazir ta samu kammala karatun da sakamako mai kyau.

Tana gurin zaune har yamma Benazir ta gama suka tafi gida a napep gurin komawarsu Benazir ta lura da yanayin Sumayyah din ta tambayeta exams dinta.

Kasa magana Sumayyah tayi sbd hawayen dasuka cika idanuwanta kafin tayi wata magana Benazir ta fahimci komai cikin damuwa da tausayin yar uwarta tayi shiru ta kasa cewa komai sbd itama tasan suna dagewa ne suyi karatun sbd azaba da hukuncin Ababa,ita kanta idan ta tina da azabar da zata biyo bayan faduwa jarabawar tashi hankalinta keyi bare Sumayyah data dandana azabar hukuncinsa na faduwan.

Shirun Benazir yasa hawayen sumayyah saukowa tana rufe fuskarta da hannuwanta sbd kukan dayake zuwar mata zuciya a karye.

Har suka isa gida kuka sumayyah din keyi itama Benazir kukan zucin takeyi jikinta a mace,

Mai napep na jiyesu suka nufi hanyar gida sumayyah na goge hawayenta dan kada hande ta gani wani masifar ya biyo baya.

Sulaiman drivern napep dinsu na aje su wayarsa ya fidda ya nemo numbern Alh bilal ya saka kira sbd umarnin daya basa akan duk yaga matsala ko damuwarsu ya sanar masa.

Kai tsaye ya sanar masa suna cikin wata matsalar sbd Sumayyah nata kuka har suka isa.

Shiru Alh bilal din yayi sbd yana tareda Mahaifinsa a lokacin.

Dan numfashi ya sauke ahankali tareda bude baci yace

 

 

 

“Ok shikenan idan na samu time zan kira naji qarin bayani.”

Kashe wayar yayi tareda ajiyewa gefensa yana qin kallon mahaifinsa sbd zai iya tambayarsa daga ina ne kiran.

Kallonsa Alhaji DAUDA KAANTE yayi sbd yasan Bilal din da zurfin ciki yanzu haka wata matsalar ce dan haka kai tsaye ya gyara zamansa kan lafiyayyar luxury couch din dayake kai cikin babban palonsa dake Kaante Mansion yace

“Da matsala ne?”

Dagowa Alh Bilal yayi ya kalli Dad Kaante yana basar da tinaninsa akan zancen kukan sumayyah yace

” ba komai bane wani yaron dana sa aka dauka aiki ne ya kira.”

Basar da zancen Dad kaante yayi cikin manyanci irin na wanda tarin arziki yagama hudawa tako ina komai a hankali kwance ba sakawa hayaniya sai ciwon kai da ‘dayan ‘dansa yake sakar masa wanda idan ba DD kaante din ba babu wanda ya isa tayar masa da hankali ya sanyasa shiga tinani.

Kallan hoton DD din da shi kadaine hotonsa ya isa a maqala a palon Dad kaante din dana Oga kwata kwata wato kakansu shugaban family din gabaki daya wanda shine Asalin Kaante din wato Dalhat kante.

Shi kansa Alh bilal hoton DD din ya kalla kafin ya sauke ajiyar zuciya cikin nutsuwa yace

 

 

 

“Dad insha Allah zan gwada masa magana zai dawo ko zuwa qarshen watan nan ne”

Numfashi mai dumi Dad kaante din yakuma sakewa a karo na ba adadi sbd ya rasa tayaya DD yake iya sakar musu pressure,

Tayaya zai dauke mahaifiyarsa da qanwarsa sama da watanni Shida suna gurinsa Zurich,

Meyasa bazaiyi tinanin anan din yaya ake ji babu su din ba,

Ina matsayin mijin Mahaifiyar tasa kuma mahaifinsa dana qanwar tasa daga zuwar masa ziyara ya riqesu,

Sam baya duba bacin Raina dana DD babba akan hakan koyaushe mahaifiyarsa kawai ya sani.

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button