Hausa Novels and Stories

Tabarma Kashi 8

Sponsored links

“Yana gurin abba,inajin dama ke yake jira tun dazun” kai ta jinjina,ya kirata a dazun sanda take zaman jiran afifa,don haka ta fara takawa a hankali zuwa hanyar da zata sadar da ita da sashen mahaifinta,baby aleena na kwance saman kafadarta

“Nazo nayi rakiya?” Afifa ta fada tana bude ledarta,ci kanki batace mata ba kamar yadda tayi zato,ta wuce abinta,sai afifan ta saki dariya tana fidda kayan cikin ledar

“Me yasa kikeso ki dinga tunzuramin qanwa ne afifa?,za’a ji kanmu fa” anty farheen ta fada dukka idanunta akan afifa bayan maama ta miqe zuwa dakinta dauke da ledar kayan da farheen din ta kawo mata kyautarsu,fuskar farheen din a sake ta yiwa afifa tambayar. Ta buda takeaway dinta ta saka fork a ciki tana dariya

“Abun sãahar ne anty kamar sake gaba yake,duk waje idan akwai maza suka wuce uku saita sakawa gurin karan tsana?,me yayi zafi haka?” Kai farheen ke gyadawa a hankali idanuwanta akan afifa,ta bude baki a nutse tace

“Babu halittar dake saurin ruguza dukkan buri mafarkai yadda da aminci na diya mace irin halittar da namiji,idan ta dace da abokin rayuwa na gari……sai kiga tana yiwa maza dukka kallon abu daya,hakanan idan aka samu akasi shima haka abun yake,a dukkanin kafatanin rayuwa kuma babu abinda yakai ciwo irin cin amana ha’inci ko yaudara daga wajen wanda ka miqawa dukkan yarda aminci da kuma qauna,a maimakon ka samu ninkin abinda ka bayar…..ko ka samu koda ace kwatankwacinsa ne, a’ah……sai ka samu akasin dukkan abinda kai din ka miqa,ba kowanne yanayi muke fahimta ba…..har sai lokacin da muka samu kanmu a kwatankwacin irin wanna hali ko yanayin” kai afifa ke gyadawa,maganganun farheen sun shigeta,musamman daya kasance kamar wani tuni ne ta sakewa afifa bawai kuma don afifan ta manta ba,a’ah…..don dai kawai zuciyarta ta kwadaitu dason ganin wasu abubuwa masu kyau na wanzuwa cikin rayuwar sãahar din tata,gyara zamanta sosai afifa tayi tana fuskantar farheen tana kuma ajiiye meatpie din hannunta data gutsura saman dan qaramin farantin tangaran din data kirayi baaba sa’a ta kawo mata,ta kawo seriousness ta dora saman fuskarta,da gasken gaske abinda bakinta zai furta a yanzu yana daya daga cikin abubuwan da ya shiga list na burikanta a yanzu

“Amma anty……shikenan sanadiyyar kuskure ko son zuciyar wani sai kabi ka kashe taka rayuwar?,saboda wani laifi na wani can mutum guda sai ayiwa kowa kudin goro a tsundumashi cikin matsalar da babu ruwansa?,matsalar da baisan da wanzuwarta ba?” Kai farheen ta girgiza,bata kai ga cewa komai ba afifa ta dora

“Mahmud abba gana fa anty……. bakiga cin kashin da taso yi masa ba yau,don kawai yayi mata magana” tun kafin afifa ta qarasa farheen ta fidda dukka idanunta waje tana dubanta cikin yanayi mamaki matuqa da gaske

“How comes afifa?” Dukka kafadunta ta dage tana yarfa hannu,alamun abun itama sam bai mata dadi ba

 

 

 

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button