Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Hausa Novel Chapter 66

Sponsored links

Tasowa yayi da sauri yana kakkabe jikinsa, cikin jin haushi shima yace;

“Kai ya kamata in tambaya ina zaka kaimin mata, dagayin tafiyar kwana biyu shikenan saiku sata a gaba?, bame tabamin ita ya zauna lafiya wallahi!!!”….

“Ji wani shashasha mahaukaci, a masallacin ubanwa aka daura muku auren da zakace matarka ce, kai dalla ware dan wallahi ka bari na fusata sai na zubar maka da hakoran gaba duka, ba kunya ba tsoron Allah kazo kuna claiming matar mutane!”….

Deen ya fada yanajin kamar ya daddalla masa mari, saidai bata wannan yake ba, burinsa kawai ya gudu da yarinyar kafin sameer ya dawo, gashi wani dan iska yazo ze rena masa hankali ya bata masa lokaci …..

“Idan kana san rayuwarka ka bani matata mu tafi”…..

Deen besan sanda ya zabga masa wani wawan mari tsabar bacin rai jin ya kara maimaita kalmar matarsa ce, ko a gidan ubanwa aka daura musu aure oh……..

Wata muguwar dariya ya fashe dashi yace….

“Ni ka mara? Hhhhh karshen ka yazo yaro”…

Wani marin ya kara masa dan ba karamin haushin dariyar yaji ba, sannan cikin masifa yace;

“An kara maka wani, do your worst karamin dan iska kawai, now bani hanya!”….

Yana fadin haka ya shige mota yasa lock, kokarin tada motar yayi mota tace to tadani kagani, babu kalan dabarun da beyiba amma shiru mota taki tashi, jin yana juyo dariyar dan iskan chan ne yasasa whining glass dan yaga meyake yiwa dariya….

Yana bude glass din ko yajuyo shi yana fadin;

“Hhhhhh kai ka dauka zaka mareni har so biyu kaci bulus? Inaaa, ai in fadamaka kome zakayi motarnan bazata tashi ba, bama motar ba babu inda zaka iya motsawa daga nan inba bani matata kayi na tafi ba”…..

Wani agogon sameer me tsada da yake cikin motar Deen ya dauka ya cilla masa a goshi, a take goshin ya fara zubar da jini, murmushi Deen yayi yace;

“Ka kara kiranta matarka a gurin nan wallahi saina kasheka, na kuma kashe banza a banza! Wato kai shedani ko? Toh ko bude idonka da kyau kaga yanda zan bar gurinnan da ita akan idanunka, duk shaidancin da kakeji dashi na fika wallahi”……..

Sai kuma ya kalli fatima zainab ya harareta yana fadin;

“Ashe a cikin kwashe kwashen naki harda shaidani? Ba dole kita abu kamar mara hankali ba, zamu gamu ne in kika farka, saina saitaki da kyau kafin in kaiki gun iyayenki!”..

Sai ya maza ya zuge glass dan bayason jin abinda wanchan wawan zece, wani cassette din Quran yasaka ya kunna suratul baqarah yayi bismillah ya sake tashin motar, cikin ikon Allah ko motar ta tashi, figarta yayi a guje ya bar wanchan da sakekken baki………

Kuka yakeyi sosai cike da nadama, tsugunawa yayi har kasa yana basu hakuri akan su taimakeshi su rufawa masa asiri…..

Mami kuwa har lokacin bata gama dawowa daga shock din data shiga ba, she always know Deen as a stubborn person amma bata dauka rashin jinsa ya kai haka ba, wani kalan hatsabibin yaro ne Allah ya bata haka? Like how could he even think of this? To ina ya tafi haka…..

Dawowa daga tinanin tayi jin Umm na fadin;

“Idan zaka fadamin gaskiyar abinda ya faru na kumayi bincike na tabbatar gaskiya ne, I’m assuring you that abinda ze sameka”…

Da sauri cikin kuka yace;

“Wallahi zan fadamiki, bazan yi karya ba”…

“Good, now tell me how you got here, in full details!”…..

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button