Latest Updates

Wace Ce Ita Hausa Novel Book 2 Chapter 10

Sponsored links

Rokonsa tayi ya kunna mata dan a kunne take ake aikota ta siyo, ba musu kuwa ya kunna mata ya bata……

Dawowa uncompleted building din data tashi tayi, kalle kalle ta hauyi taga ko me taban yana ganinta, ganin baya hangota yasata gyara zama sannan tashiga busa sigarin, zuka take ba kakkautawa tana fatan zataji sanyi a ranta saidai inaa kamar kara mata abinda ke damunta akeyi….

 

Cillar da guntun daya saura tayi tana dana sanin sha dan shanta na uku kenan amma ta kasa gane dadinsa shiyasa tayi sticking to syrup datasan inta sha ze bugar da ita a take yasata bacci ko banza zata manta duniya da damuwar dake cikinta…….

A nitse yake driving har yasha kwana ya shiga street din, a fizge ya hango kamar mutum a jikin sabon ginin da akeyi a unguwar inba kizo idonsa ke masa ba kamar kuma mace ce yarinya karama, kasancewarsa mutum me tausayi sai ya kasa hucewa, dawowa yayi yayi parking a daidai inda take, alama ya shiga mata data taso saidai sam bata gane abinda yake nufi ba, tana dai kallonsa amma batasan me yake cewa ba, fitowa Alhaji Ibrahim yayi daga motarsa ya karasa inda take……

Alhaji Ibrahim ya tambaya yana namakin yanda take sanye da sitirun arziki amma aika tau take, koda yake ai shugabanninsu suna basu kaya, hakan yasa ya kauda tinanin……

“Eh!”…..

“Waya kaiki gidan aikatau din?”…

“Nina kai kaina!”…

Jinjina kai daddy yayi yana mamakin wannan izza tata gashi daga gani she’s smart shine zaa bar yarinya ba karatu wai aikatau ta kai kanta, shi kuma gashi mutum me balakin son karatu, a take yaji yanaso ya taimaketa ya inganta mata rayuwarta…..

“Kiyi hakuri wata rana sai labari, taso muje kinji ko?”……..

Ba musu ta mike ta bishi dan har a lokacin bata cikin hayyacinta…….

Shida yazo da niyar zuwa ya gaida amininsa sai gashi yayi reverse ya koma da ita gidansa……..

Tinda suka dau hanya yake mata tambayoyi akanta, amsa take bashi kawai batareda tasan me take fada ba, shikuma ya hau ya zauna akan duk abinda ta fadamasa dan dagaske a yanayin maganarta bazaka gane a bige take ba…..

Suna zaune a main parlor suna jiransa dan tin kafin ya karaso ya kirasu yace su jirasa a parlor gashi nan…..

Hade baki sukayi wajan amsa sallamar Alhaji Ibrahim dayake tafe da yarinyar da basu gane wacece ita ba…..

“Yauwa sannunku, wannan yarinya a kula da ita a bata abinci taci, bari naje nayi sallah na dawo”…..

Yana fadin haka ya fita daga parlourn……

“Kutumar uba mu Alhaji ze renawa hankali, ya sunkuto zukekiyar yarinya kamar wannan yace mu kula da ita kamar marasa aikin yi? Allah ya kiyaye wallahi!”….

Budar bakin mama(hafsah) kenan bayan fitar alhaji daga parlourn……

“Wasa ma yake wallahi, ba bayani ba komai kazo ka ajye mana yarinya kace ka tafi masallaci?”……

Momma(maman khaleel) ta kara da hakan…..

“Ke wai baki iya gaisuwa bane?”….

Cewar mama da abun yafi damunta kasancewarta mutum me zafin kishi…..

Kallonta rashin fahimta fatima zainab ta mata dan bata gane me take cewa ba saboda wani bacci daya fara fuzgarta a gurin, a hankali tace;

“Tohhh”…..

“Wace irin fitsararriyar yarinya alhaji ya kwaso haka? Ina ce miki kiyi gaisuwa kina cemin wani tohhh”……

“Yausheee?”……

“Ikon Allah kin jimin yarinya maganar da nake daban abinda take fada daban!……

“Hafsah anya yarinyar nan baa bige take ba kuwa? Kigafa yanda take magana kamar ki tureta ta fadi”…..

“Babu tantama a bige take, toh wallahi bazata sabu ba, yazo yaga abinda ya kwaso dan baze kwaso abinda ze lalata mana tarbiyyan yara ba”……

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button