Hausa Novels and Stories

Nihad Chapter 9 Hausa Novel

Sponsored links

Nihad na shesshekan kuka tace “Wllh shi inna, kawai an bar sa yana ta abinda ya ga dama a gidan kamar gidan ubansa, duk ya gama rena ni, ko gaisuwa bata hadani da shi” Inna tace “Duk ba wannan ba, yanxu kin kira Aliyun??” Nihad ta daura kanta gefen gadon inna hawaye na sauka idonta tace “Bayan ya ki dagawa” Inna ta dauko wayarta ta mika mata tace “Kirasa da nawa” Nihad tace “Ae idan ba shi da numberka baxa ka iya samunsa ba, ya sa layinsa a Private” Inna tace “Wai ko ba dai Aliyu ɗ’an wajen janaral Habubakar jikamshi ba?” A hankali Nihad tace “Shi…” Inna tace “To wannan dreba duk yanda aka yi tsinanne ne, ko don nace masa ya saki jikinsa yasa ya sake kamar gidan ubansa? to ai ni na xata yaron arxiki ne” Salati inna ta saki tayi tagumi tace “Yau naga dreban jaraba, ashe duk ni na ja komai da nace ya saki jikinsa, to a kira min Ibrahim din tun yamma bai yi ba ya sallamesa” Nihad ta dau wayar inna da sauri ta fara neman number Abba tayi dialing, Inna ta bude baki ta rike ha6a tace “To shi kuma Aliyun banda abunsa garin yaya xai ce sai yayi ma dreba magana mutumin da ba ajinsa ba, ai abinda bai sani ba talakawan nan haka suke da dacin rai kamar mutum ne ya doro masu talaucin, ina shi ina wani basamuden buzun dreba can?

 

To ko a almajiri dai baxa su yarda su ajiye wannan mutumi a gidansu ba balle dreba, su da tun daga titin da ya yanka unguwarsu xaka fara ganin dirka dirkan sojoji har da motocinsu….” Nihad ta turo baki tace “Abba bai daga ba” Inna tace “Ina xai daga, ya tashi ya kawo wani kato gansameme kamar mutanen farko ya dau mota ya basa, ni wllh ranan da na fara ganinsa sai da na tsure, sai fa ya daga mutum ya nanasa da kasa sau biyar bai gaji ba, irinsu ai gadin dogon banki ya kamata a basu ba wai motar mutane ba” Nihad dai tayi tagumi don abinda ya dameta daban, ita yanxu ta ya xata fara shawo kan Aliyu, da yaya ma suka dawo soyayyar, Inna tace “To ko kin san inda ya sauka ki rakani mu je in basa hakuri” Nihad ta kalleta tace “Ji ki kuma, kawai don ki ja min raini?” Inna tace “Wani raini mutumi na nema ya kubuce, wa ke ta wani raini Nihad, idan ma baxa ki shiga ba ni ki rakani ki nuna min hanya in je in samesa” Nihad tace “Aa ke dai kawai duk yanda xa kiyi kiyi Abba ya kori driver din nan kawai” Inna tace “Yo sai ma kin fada, abu har ya kai yana korar ma jikokina samari”

 

Hamid ne ya bude kofar dakin ya shiga yana kallon Nihad yace “Ke don uwarki ni sa’anki ne xaki wuce ni da abokina baki gaishemu ba” Nihad ta turo baki ta koma gefen Inna, Inna dai bata ce komai ba, Yace “Mahaukaciya kawai, uban wa xaki dinga daga ma kai?” A fusace Nihad tace “Kina dai gani babu abinda na masa ya xo ya fara xagina ko inna, ni fa shi yasa bana son xuwa gidan nan wllh, kowa yaje yaji da mugun halinsa” Cikin xafin nama ya nufeta, Inna ta mike ta wangale hannu tana tare Nihad tace “Dokeni to, Hamidu nace ka dokeni” Huci yake yana kallonta, Inna tace “Ai dama ka saba dukan nawa yanxun ma ka duka, ranan da ka biyo Bilkisu ai ni ka jibga ba ita ba” Nihad ko kallonsa bata yarda ta sake yi ba, Yayi wani kwafa ya fice daga dakin, Inna ta kulle dakinta tace “Kinsan korosa aka yi daga can kasar wajen wai wa’adinsa ya kare a can, to kuma sai kayi ta hucewa kan ya yan mutane” Nihad bata san lkcn da ta kyalkyale da dariya ba, Inna tace “Allah haka uban yace min, duk a booth din jirgi aka kwaso su aka dawo” Nihad dai bata ce komai ba, Inna tace “Yanxu ko kin boye number ki baxai daga wayar ba?” Nihad ta mike tace “Ni dai xan tafi inna dama anjima da daddare kice Hamid din ya kawoki nan gidanmu ki samu Abba da kanki” Inna tace “Toh shkkn ma, kawai bari inje in riskesa a gidan ba sai mun yi waya ba, idan ma ya kama ko shi sai ya kira Aliyun ya basa hakuri” Bude baki Nihad tayi, can ta kyabe bakin tace “Ni dai sai kin zo” Daga haka ta fita daga dakin, A bakin gate abokin Hamid ya tare ta da ya faki idon Hamid ya biyota, yana fara magana ta dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu tana yatsine fuska tace “Ina wasa da kai ne malam?” Daga haka ta ja tsaki tayi ficewarta daga gate din, ya bi ta da kallo baki bude, dama Hamid ya gaya masa ya ki ji. Nihad na komawa anguwansu ta yi ido hudu da Khalil dake xaune kan dakali a kofar gida wayarsa na kare kunnensa, yana ganinta bai sake cewa komai ba a wayar da yake kuma bai cire wayar a kunnensa ba, har ta isa dai dai inda yake, tayi masa wani harara ta ja tsaki ta shige cikin gida tayi banging gate din. Abba na tsaye balcony bayan magrib Khalil ya karaso da ladabi yana kallonsa yace “Gani Alhaji” Abba yace “Yauwa pharmacy xan aikeka ka siyo min magani yanxu” Khalil yace “Toh, ya sunan maganin?”

 

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button