Hausa Novels and Stories

Wace Ce Ita Book 2 Chapter 63

Sponsored links

Kamar a mafarki ya hangota tana saukowa daga kan step sadap sadap jikinta sai motsawa yake a cikin silk rigarta, murza ido yayi dan ya tabbatar ita din yake gani ko kuwa, mamaki ne ya kamasa ganin da gaske ita dince, sake baki yayi yana kallonta kamar ya hadiyeta daga zaune, sosai ta mishi kyau kamar ya saceta ya boyeta yana ganinta ita kadai, ya rasa meyasa kome tasa yake mata kyau, ga bakinnan sai maiko yake yana daga masa hankali, kasa jurewa yayi ya zaro wayarsa ya hau yi mata hotuna da videos, ita ko batasan yanayi ba dan bata ma ganshi ba, burinta kawai ta fice batareda kowa ya sani ba, deen kuma yanaso ya dakatar da ita amma inaa hankalinsa ya riga ya gushe a wajan kallonta, saida ta kai daidai bakin kofa yaji kamar an tsikaresa, da sauri ya ajye wayar ya daka mata wani mugun tsawa yace;

“Kehhhhh!!!!”…..

Har ta dora hannunta zata bude kofa taji muryarsa ta daki kunnenta, a gigice ta cire hannunta daga kan kofar ta juyo tana neman inda yake, sai a lokacin ta gane yana parlourn tin data fito kenan…..

 

Wayarsa ya dauka yana kallon hotunan daya mata a cikin wayar a dake yace;

“Sai ki jira in kunyi shashashan auren sai ku fita ko tsakiyar dare ne, now koma ciki mara kunya fitsararriya!!!”……

 

“Yana fa waje yanzu, bari inje ince mishi ya bari gobe toh”…..

 

“Wai me yake damun brain dinki ne zahrah? When will you start differentiating between right and wrong? Kin cika turare kamar kampanin turaren ne zakije gurin saurayi? Kalli kayan dake jikinki dan Allah? Haka zaki tafi kina tallan jikinki ko wani jack and jill ya kalla kenan?! Mayafin kuma da kinsani cillarwa kikayi dan dashi da babu duk daya, bansan meyasa mami da umm ke barinki kina shiga anyhow ba, zaki wuce sama ko sai na karya miki kasusuwa?, stupid girl kawai!”….

 

Deen ya fada cike da takaici, shi yanzu baya ma ganin lefinta sosai, umm da mami ne suka barta take saka matsattsun kaya, toh wallahi za’ayi yaki dashi a gidan nan akan haka dan baze lamunta ba…..

 

Kamar zatayi kuka ta marairaice tace;

 

“Yaya dan Allah koda 5mins ne in fita mu gaisa kaga babu dadi yazo kuma ince ya tafi bamu haduba”….

 

Wayar da yake hannunsa ya saita daidai bakinta daya iya tsara kalamai idan yaso, harda wani yayan munafurci, sanda yake binta tace masa yaya ai ki tayi sai yanzu saboda wani gardi, ba shiri ta matsa wayar ta fadi ta fashe a take, sai kuma taga ya nufota gadan gadan, da sauri ta kwasa a guje tayi sama, bedroom din daya koma mallakinta ta shige da sauri ta rufe kofa…

 

Kwafa yayi ya dauki wayarsa daga kasa, kallon screen din yayi yaja tsaki yace;

 

“Foolish girl kinyi min asarar pictures dinki, dole ma in gyara wayar!”…..

 

Zira wayar yayi a aljihunsa ya haura sama, be bi takan bedroom dinta ba ya shige na umm, be sameta a ciki ba sai ya tafi na mami, knocking yayi ya shiga bakinsa dauke da sallama, amsa masa mami da umm dake tattaunawa sukayi, mami zatayi magana yayi saurin rigata da fadin;

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button