Hausa Novels and Stories

Jinkirin Aure Complete Hausa Novel

Sponsored links

Iska ce ke kaɗawa ta damuna me cikakken sanyi da sanya zuciyar da take cikin kwanciyar hankali a nishaɗi, yayin da zuciyoyin da suke cike da zullumin damuwa suke kasancewa da sassaucin yanayi.

 

Saidai a gurinta itan wannan yanayi yafi mata kowanne yanayi zafi, rayuwarta ta ƙuntata hawayenta ya yawaita ƙuncin zuciyarta ya ƙaru a yayin data keɓance kanta ita kaɗai a madaidaicin office ɗin nata me ɗauke da table me kujera ɗaya, gabanta cike yake da files-files na petiant ɗinta na yau data gani inda gabadayan hankalinta yabar gangar jikinta a zaune saman kujerar lokaci zuwa lokaci hawayenta ba diga saman takardar dake gabanta.

 

Ƙwankwasa ƙofar akayi har karo uku dake hankalinta baya jikinta batasan anayi ba, jin shirun ne yasa me neman izinin turo ƙofar tare da sallama ta shigo cikin office ɗin ta tsaya ta zubawa Mamallakiyar office ɗin idanu tana mamakin abinda yake sanyata shiga matsananciyar damuwar da har hankalinta yake gushewa haka.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Dukan Table ɗin Dr Zaheera tayi abinda ya dawo da wadda ke zaunen cikin nutsuwarta tayi saurin sa handcap ta share idanunta ta ɗagosu ta zubasu kan Dr Zaheera itama ita take kallo harta isa ga wata kujerar ta zauna suna facing ɗin juna.

 

Dr Zahira ce ta kawar da shirun da cewa “Kullum kin kasance cikin damuwa kin takuri kanki kin tsawwala kanki Dr Madinah meye yasa hakan ne? Meyesa kike mantawa duk abinda ba’a fareshi akanka ba bazaa ƙare shi akanki ba?”

 

Manyan fararen idanunta ta lumshe ta kwantar da kanta saman kujerar da take kai hawaye na tsiyaya daga kwarmin idanunta tasa tisue ta goge dogo hancinta

 

“Meye ne matsalata meye ne aibina meye yasa kyawuna ya kasa samar min da mijin aure, meyesa kullum al’umma basamin adalci suke ganin cewar nice naƙi aure bayan Nima nafi kowa son na ganni cikin dausayin sunnar ma’aikin Allah???

 

Tambayar da kullum nakewa kaina kenan”

 

 

 

 

 

 

 

Cewar Dr Madinah dake ɗagowa tana zuba idanunta akan ƙawarta Dr Zahira, shiru Dr Zahira tayi na ɗan lokaci sannan ta buɗe baki tace.

 

“Dr Madinah ba jama’ar gari da suke ganinki daga nesa ba ni kaina da nake da kusanci dake lamarinki yana bani mamaki gani da sani a damuwa da tunanin meye dalili? Madinah kyawunki yakai ace kina juya ragamar maza a hannunki sai kuma ya kasance maza sune ƙaddararki, ta yaya zan yarda ace mu da bamu kai ba maza na zumuɗi akanmu ke da kika wucce kice babu wanda ya taɓa cewa yana sonki?”

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Murmushi me ciwo Madinah tayi tana kai dubanta ga agogo ta miƙe ta fara harhaɗa files ɗin ta sanyasu wajen adanasu ta ɗauki jakarta ta dubi Dr Zahira tayi gaba tana cewa “duk sanda na tsaya tuntuntunin abinda kike tunani yanzu Zuciyata zafi takeyi Zahira ni kaina na fara tsoron kaina ina tunanin to ko wani abune ke gareni abin gudu da Ni na kasa ganewa, Zahira shekaruna sun fara tafiya a matsayina na ɗiya mace ba namiji ba ace na zubar da shekaru talatin da biyu batare da aure ba wannan abu da cin rai yake…..”

 

Isa sukayi bakin titin suka tari ɗan sahu suka hau ya fara sauke Zahira a kwanar unguwar su sannan ya wuce da Madinah tasu unguwar ya sauke ta ta fito tana gyara mayafin data yafa saman uniform ɗinta na aiki ta nufi unguwar tasu lokaci zuwa lokaci suna gaisawa da dattijan unguwar dake zaune a ƙofar gidajensu.

me gunji tare da kifa kanta a kafaɗar Ammi, cike da tausayawa Ammi ta shiga bubbuga bayanta da sanyin yanayi na mahaifiyar da taga ɗanta cikin halin tsanani tace “Shikenan Munau na fahimceki ki daina kukan haka Allah yanaji yana gani zai kawo mana mafita da yardarsa zanci gaba da yimiki addu’a kema karki gajiya wannan ita ce ƙaddarar mu, yawwa ɗazu baffan ku Sunusi yazomin da maganar haɗin aurenki da ɗan uwanki Khamal…”

 

A firgice ta ɗago tace “Ni kuma Ammi habadai Khamal kin manta waye Khamal Ammi ƙungurmin ɗan taba sannan ɓarawon kaji da awakin unguwa ace shine mijina? A’a nikam wannan zaɓin baimin ba nidai a tayani da addu’a nasan Allah bai manta dani ba Ammi”

mukeja ake zaginmu ana cewa mun ɗaure Miki gindi kina yawo da sunan karatu ni wani lokacin gwiwata har sanyi takeyi”

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Kwantar da kanta tayi jikin bedside tace “kuyi hƙr No condition is permanent Ya Mus’ab wata rana sai labari Allah shaida ne bana aikata abinda mutane suke zargina dashi Yaya duk wata mace da wannan ƙaddarar ta faɗa mata dama sociaty dinmu kallon ƴar iska gantalalliya watsattsa sukeyi mata hatta da Allah ya hukunta zai aureta bayajin a ransa budurwa zai aura, nifa da wannan surutun da nakeja muku wlh ko za’a bani sadakin bazawara indai nagartar mijin takai gara na karɓa indai yayi albarka Shikenan”

 

 

 

 

 

 

 

Murmushi yayi ya miƙe cike da tausayin ƙanwar tasa yace “Insha Allahu komai zai wucce ki kwanta goma ta wucce gashi gobe talata” fatan alkhairi tayi masa ya fice tare da ja mata ƙofar ta miƙe tayi mata key ta shiga bayi ta dauro alwata ta kwanta daidai lokacin da aka kece da wani ruwa me ƙarfi ta kunna MP tana sauraron ƙira’a tare da tsunduma duniyar tunanin rayuwar baya.

 

Kamar yanda ta saba yauma ganin zata raba dare bacci yakasa ɗaukarta tana hasaso lkcn da zata kwanta kusa da mijinta ta tayi matashin kai da ƙirjinsa ta shafa sumarsa taja gemunsa, wannan rana ji takeyi dama zata iya kissimo irin nishaɗin da zata kasance dama tazo mata nan kusa dama zata buɗe idanu taga ba ita ce Madinan da abu ɗaya ya zamewa tsaiko cikin rayuwarta ba.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

To wai meyene abinda ya zame mata katanga da samun abokin rayuwa ne? Tambayar da kullum takewa kanta da makusantanta kenan amma ta kasa samun amsa saidai ace mata tayi hƙr lokaci ne idan ta hƙr ta cire komai a ranta kuma sune waɗanda zasu fara cewa da ita “Madinah wai yaushe zakiyi aure ne?” Wannan tambaya tana dagula lissafin ta da ace mutanen duniya zasusan ƙuncin da take shiga a dalilin wannan tambaya da sun daina yi mata ita.

 

Zuwa yanzu abubuwa sun fara yi mata nauyi sha’awar kasancewa da namiji abokin ɗebe kewa tana yawan bijiro mata takan raba tsayin dare bata iya bacci ba saboda ciwon mara idan abin ya ta’azzara har fita takeyi daga hayyacinta sai likita ya tsaya a kanta sannan take dawowa daidai.

 

Sai bayan sallar asuba sannan ta koma ta kwanta bacci me nauyi ya dauketa dake yau ba itane da dutyn safe ba tanada isasshen lokacin bacci ba ita ta farka ba sai 12:21pm ta farka shima tashinta akayi ta buɗe idanunta kan Ƙawar tata kuma abokiyar aikinta Dr. Zahira murmushi sukayiwa juna Zahira tace “Tunda nayita kiran wayar ki najita a kashe nasan kinanan kina sana’ar saiki tashi mu fita inaso zaki rakani unguwa”

Sponsored Links

Leave a Reply

Back to top button